Rahoto

Matawalle ba tsararka ba ne – APC ga Gwamna Dauda

Matawalle ba tsararka ba ne – APC ga Gwamna Dauda

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam'iyyar APC ta Jihar Zamfara ya yi Allah wadai da sanarwar da Gwamna Dauda Lawal ya yi a kafafen yaɗa labarai kwanan nan da ake zargin ya bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu sharaɗin ya kori ƙaramin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle kafin ya koma jam'iyyar ta APC. Sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar Yusuf Idris ya yi wannan sanarwar a cikin wata sanarwa da ya fitar wa manema labarai a Gusau a yau Alhamis. Jam'iyyar ta yi Allah wadai da yadda Gwamna Dauda ya ya ɗauki Matawalle a matsayin babban abokin gabar sa da…
Read More
Al’ummar Nufawa da kafuwar Masarautar Nupe a Nijeriya (II)

Al’ummar Nufawa da kafuwar Masarautar Nupe a Nijeriya (II)

Kamar yadda jaridar Blueprint Manhaja ta fara kawo wa mai karatu tarihin asalin Nufawa a makon da ya gabata, a wannan makon za ta cigaba daga inda ta tsaya. Masarautar Bida ta zama ta farko a lokacin Turawan mulkin mallaka, a lokacin ’yancin kan Nijeriya sarakunan ƙasar Bida sun ba da gudunmawa wajen haskaka bikin ’yancin ƙasar nan. Har zuwa yau, masarautar Bida na shirya bikin gargajiya da ake wa laƙabi da ‘Nupe Cultural Day’ don tunawa da gudunmawar da sarakunan masarautar suka bayar da ake wa laƙabi da ‘Etsu’. Sarakunan ƙasar Nufe daga shekarar 1531 zuwa 1835: Tsoede, wanda…
Read More
Ƙiba da matakan guje mata – Kashi na biyu 

Ƙiba da matakan guje mata – Kashi na biyu 

Gabatarwa Ƙiba na nufin adadin kitse da ya wuce yadda ya kamata wanda ke haddasa illa ga lafiya. Mata da dama suna ɓata lokacinsu me tsada kan neman hanyoyi da za su rage ƙiba wanda wasu hanyoyin masu ɓullewa ne amma wasu kuma masu illa ne ga lafiya. Babban dalilin zaɓen wannan batu ana ganin kiba ba wai kawai lafiyar jiki ba, har ma tana shafar ƙwalliya (skin, fata), saurin tsufa, ƙwarewar rayuwa (self-esteem) da yanayin zamantakewa duka ta shafa, wanda mata su suka fi faɗawa wannan damuwar. Tsarin abinci (Sample Diet Plan) da hujjojin likitoci: Babban matakin rage ƙiba…
Read More
Yaƙi da ƙwaƙwalwa

Yaƙi da ƙwaƙwalwa

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Ba fa a banza Allah ya yi kiran a yi amfani da kwakwalwa, wato a rika tunani, nazari, bincike, duba, kallo (tadabburi iri-iri) a wurare sama da 800 cikin Qurani ba. Umarnin da ya zarta kowane irin umarni hatta na sallah da zakka da aikin hajji. Dalili shine amfani da kwakwalwar da Allah ya huwace mana shine ya banbanta mu da duk sauran halittu a duniya, kuma abinda ke tabbatar da Imani wajen banbance gaskiya da bata, ci gaba da koma baya, nasara ko akasinta. Ba a harkokin Imani kadai ba, hatta a harkar yau da…
Read More
Gwamnonin Nijeriya shida da suka taɓa zaman kurkuku a Nijeriya

Gwamnonin Nijeriya shida da suka taɓa zaman kurkuku a Nijeriya

Cin hanci da rashawa na daga manyan ƙalubalen da suka addabi Najeriya tun bayan dawowa tsarin dimokuraɗiyya a 1999. A 2012, an kiyasta cewa ƙasar ta yi asarar sama da dala biliyan 400 tun bayan samun ‘yancin kai. A bisa rahoton Transparency International na 2024, Najeriya ta samu maki 26 cikin 100 a jerin Corruption Perceptions Indeɗ (CPI) — ɗan ɗigogi sama daga maki 25 da ta samu a 2023. Har yanzu an saka ta a matsayin ƙasa ta 140 cikin ƙasashe 180, lamarin da ke nuna matuƙar yawaitar cin hanci a sashen gwamnati. Ko da yake an samu ɗan…
Read More
Farfesa Barnabas Barde ya gabatar da laccar jami’ar Nasarawa karo na 56

Farfesa Barnabas Barde ya gabatar da laccar jami’ar Nasarawa karo na 56

Daga JOHN D. WADA a Lafia An shawarce masu harkokin kasuwanci a faɗin ƙasar nan baki ɗaya su zuba jari sosai a fannin fasahohi domin su taimaka musu wajen ɗorewar harkokinsu na kasuwanci da kuma inganta ayyuka da nasarori. Shawarar ta fito ne daga wani malami a sashen gudanar da kasuwanci na Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, Farfesa Barnabas Embugus Barde. Farfesan ya kuma shawarce su da su riƙa koyar da ma’aikatansu yadda za su yi amfani da sabbin fasahohin zamani yadda ya kamata, domin taimaka wa kasuwancinsu kawar da tsofaffin dabaru da kuma samun karin yawan aiki cikin…
Read More
Wurin Mauludi waje ne da ake ƙara son Manzon Allah, inji Sa’idu Ahmad

Wurin Mauludi waje ne da ake ƙara son Manzon Allah, inji Sa’idu Ahmad

Daga SULEIMAN HUSSAINI D/KUDU a Kano An bayyana wajen da ake gudanar da Mauludi da cewa wuri ne mai matuƙar muhimmanci da ake ƙara nuna soyayya da kauna ga Manzon Allah (SAW), tare da koyon kyawawan halayensa domin samun rahamar Allah (SWA). Wannan furuci ya fito ne daga bakin fitaccen malamin addinin Musulunci na garin Dawakin Kudu, Malam Sa’idu Ahmad Gidan Nagunda, yayin Mauludin Zawiyyar Gidan Nagunda da aka gudanar a makon da ya gabata. Malam Sa’idu ya ce Mauludi wata babbar makaranta ce da ke ƙara kusantar da al’umma ga Annabi (SAW), musamman matasa da yara. Ya bayyana cewa…
Read More
Ƙananan ‘yan kasuwa na Arewa sun bajekolin sana’o’in mata a Jos

Ƙananan ‘yan kasuwa na Arewa sun bajekolin sana’o’in mata a Jos

Daga HABU ƊAN SARKI, Jos A yayin da ake kukan taɓarɓarewar tsaro a yankin Arewacin ƙasar nan, musamman a jihohin tsakiyar Nijeriya kamar Jihar Filato, wasu matasa mata da ke harkar tallata kayan da suke sana'antawa a zaurukan sada zumunta, sun bayyana kansu ƙarƙashin shirin kasuwar bajekoli ta Arewa, da suka yi wa laƙabi da Arewa Festival, inda masu ƙananan sana'o'i fiye da ɗari da ashirin suka samu fitar da kayan da suke sayarwa ga jama'a a babban filin Polo na Jos. Wani abin burgewa da ƙayatarwa a taron shi ne yadda ƴan kasuwar suka fito daga ɓangarori na addini…
Read More
Haƙƙin Iyali: Ciyarwa

Haƙƙin Iyali: Ciyarwa

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Iyali na wannan mako, sannunku da jimirin bibiyar jarida mai farin jini, Blueprint Manhaja. A wannan makon, za mu tattauna kan darasin da a wannan zamani ya fi ci wa mata tuwo a ƙwarya tsayin lokaci, musamman ma a ƙasar Hausa. kafin mukai ga tattauna ƙorafin mata kan rashin ciyar da su da mazansu ke yi, bari mu fara kan mazan wanda wataƙila mu samo wata mafita ko fahimta a cikin lamarin. Akwai wani lokaci can bayan a kafar sadarwa ta ɗ wanda a baya aka fi sani da…
Read More
Rawar da kwalliya ke takawa a rayuwar matan Arewa

Rawar da kwalliya ke takawa a rayuwar matan Arewa

Daga AISHA ASAS  Kwalliya ba wai kawai man shafawa ba ce ko fentin leɓe da gashi, a'a, wata hanya ce da mata ke bayyana kansu, suna ƙarfafa gwiwarsu, suna jan hankali da kuma neman girmamawa a cikin al'umma. A Arewacin Najeriya, inda al'adu da addini ke taka muhimmiyar rawa, kwalliya ta samu wani matsayi na musamman. Amma shin me ya sa kwalliya ta zama abin alfahari ga wasu, yayin da wasu ke kallonta a matsayin kwaikwayo ko tsinuwa? A al’adance, mata a Arewa suna amfani da lalle, turare, dilka da man shafawa don ƙawata kansu. Amma zuwan zamani ya kawo…
Read More