Rahoto

Haƙƙin Iyali: Ciyarwa

Haƙƙin Iyali: Ciyarwa

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Iyali na wannan mako, sannunku da jimirin bibiyar jarida mai farin jini, Blueprint Manhaja. A wannan makon, za mu tattauna kan darasin da a wannan zamani ya fi ci wa mata tuwo a ƙwarya tsayin lokaci, musamman ma a ƙasar Hausa. kafin mukai ga tattauna ƙorafin mata kan rashin ciyar da su da mazansu ke yi, bari mu fara kan mazan wanda wataƙila mu samo wata mafita ko fahimta a cikin lamarin. Akwai wani lokaci can bayan a kafar sadarwa ta ɗ wanda a baya aka fi sani da…
Read More
Rawar da kwalliya ke takawa a rayuwar matan Arewa

Rawar da kwalliya ke takawa a rayuwar matan Arewa

Daga AISHA ASAS  Kwalliya ba wai kawai man shafawa ba ce ko fentin leɓe da gashi, a'a, wata hanya ce da mata ke bayyana kansu, suna ƙarfafa gwiwarsu, suna jan hankali da kuma neman girmamawa a cikin al'umma. A Arewacin Najeriya, inda al'adu da addini ke taka muhimmiyar rawa, kwalliya ta samu wani matsayi na musamman. Amma shin me ya sa kwalliya ta zama abin alfahari ga wasu, yayin da wasu ke kallonta a matsayin kwaikwayo ko tsinuwa? A al’adance, mata a Arewa suna amfani da lalle, turare, dilka da man shafawa don ƙawata kansu. Amma zuwan zamani ya kawo…
Read More
Musa Iliyasu Kwankwaso: Shekaru 60 masu albarka

Musa Iliyasu Kwankwaso: Shekaru 60 masu albarka

Daga SHEHU MUSTAPHA CHAJI Allah ya albarkaci Jihar Kano da mutane da suka shahara suka ɗaukaka a fannoni daban daban na rayuwa, suke kuma bada gudunmawar su domin cigaban al'umma. Hon. (Dr) Musa Iliyasu Kwankwaso yana cikin jerin kanawa da suka sami ɗaukaka da shahara a fannonin da suka zabar wa kansu dan bada gudunmawar su dan cigaban Jihar Kano da Arewa da Najeriya.Tarihin dimokuraɗiyyar mu ba zai taɓa cika ba sai an nakalto tarihin gwagwarmaya da gudunmawar Musa Iliyasu Kwankwaso.Ya kasance cikin mutanen da suka sa siyasar Kano ta zama ta daman saboda suna ƙoƙarin ganin cewa al'umma na…
Read More
Al’ummar Nufawa da kafuwar Masarautar Nupe a Nijeriya (I)

Al’ummar Nufawa da kafuwar Masarautar Nupe a Nijeriya (I)

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A yau, Jaridar Bleuprint Manhaja za ta yi duba ne kai tsaye zuwa ga asalin ƙabilar Nufawa da yadda suka fara rayuwa bayan isowarsu ƙasar Nijeriya da kuma kafuwar Masarautarsu. Nupe wasu ƙabilu ne da suke rayuwa a tsakiyar Nijeria kamar su Jihar Neja, Jihar Kwara, Jihar Kogi da Abuja, Hausawa suna kiransu da suna Banufe (ɗaya) ko Nufawa, wato masu yawa kenan. Makwaftansu Gwarawa suna kiran su da suna Anupeyi, kuma Yarbawa suna kiran su da suna Tapa (Takpa). Akwai wasu yaruruka sama da biyar wadda su ke ƙarƙashin Nufawa wato Kakanda, Dibo, Kupa, Gana…
Read More
Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi

Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnan Taraba, Agbu Kefas ya sanar da dakatar da sauya sheƙa daga jam’iyyarsa ta PDP zuwa APC a dalilin sace ɗalibai mata ’yan sakandire da aka yi a Jihar Kebbi. Gwamnan ya ce zai ci gaba da tattaunawa da kuma nazari kan lokacin da ya fi dacewa ya sauya sheƙar tare da magoya bayansa. Manhaja ta ruwaito cewa, da sanyin safiyar Litinin, 17 ga watan Nuwambar 2025, mahara suka shiga a makarantar sakandare ta ’yan mata da ke garin Maga a Jihar Kebbi, inda bayanai ke nuni da cewa sun yi awon gaba da…
Read More
Gwamna Yusuf ya ɗauki masu gadi 1,600 aiki don kula da tsaron makarantu a Kano

Gwamna Yusuf ya ɗauki masu gadi 1,600 aiki don kula da tsaron makarantu a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da tura sababbin ma’aikatan tsaro na makarantu 1,600 zuwa makarantun sakandare a faɗin jihar, a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa tsaron makarantun jihar. Matakin ya biyo bayan sace ɗalibai mata 25 da aka yi a Jihar Kebbi kwanan nan. Gwamnan, a ranar Talata, ya ƙaddamar da rabon takardun ɗaukar aiki na dindindin ga sabbin ma’aikatan. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu, Gwamna Yusuf ya bayyana wannan mataki na tura jami’an tsaron makarantu da yawa a lokaci…
Read More
Tasirin man kaɗanya a lokacin sanyi

Tasirin man kaɗanya a lokacin sanyi

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin kwalliya na jarida mai farin jini Manhaja, sannunku da jimirin bibiyarmu. Kasancewar sanyi ya fara kunno kai, za mu fara karkata a ɓangaren ababen da ke taimakon fata don fuskantar wannan lokaci cikin sauƙi. Kamar yadda kuka sani, shafin Kwalliya na tafiya daidai da lokaci ne don amfanin masu karatu. Kafin komai bari mu fara da bayanan masana kan irin abinda yake cikin man kaɗanya na daga sinadarai. Masana sun tabbatar da samuwar fatty acids a cikin man kaɗanya, wato wani sinadari da ke gina fata. Samuwar waɗanan fatty…
Read More
Dandalin shawara: Mijina ya nisanta kansa da zama uban cikin da ke jikina

Dandalin shawara: Mijina ya nisanta kansa da zama uban cikin da ke jikina

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS  TAMBAYA: Aisha Asas barkanki da yau. Ya jama'a dai. To madalla. Don Allah ki taimaka min yadda ki ka saba ba wa mutane shawara da suke amfana da ita har ta yi masu aiki ga abinda yake ta damun rayuwarsu.  Kina ji na ko, wato miji ne nake tare da shi da ban san kowanne irin mutum ne ba, ya sani duk daren Allah sai ya...........(mun cire kalmomin saboda rashin dacewar ta). Kuma kar ki ce sau ɗaya, har ba iyaka. To wai yanzu na yi ciki, asibiti an ce Ina ɗauke…
Read More
Tweakrr: Yadda ’yan Nijeriya suka ƙirƙiri fasahar AI da ke sauya fannin bincike a duniya

Tweakrr: Yadda ’yan Nijeriya suka ƙirƙiri fasahar AI da ke sauya fannin bincike a duniya

Akwai lokuta a rayuwar ɗan adam da wahala kan haifi abin mamaki, da kuka kan zamo dariya. Wannan shi ne labarin yadda wani dare mai duhu a rayuwar ɗan Nijeriya ya zama hasken sabuwar fasahar da ke sauya duniyar bincike gaba ɗaya. A lokacin da Kamil Bello Furƙan ya rasa aikin bincikensa da ya shafe watanni yana rubutawa, bai san cewa asarar nan za ta haifi abin da zai girgiza duniya ba. Amma da ya haɗa kai da abokinsa Lawal Habeeb, suka ƙirƙiri Tweakrr — wata sabuwar manhajar basirar wucin-gadi (AI) wadda ke yin abin da babu wata fasahar da…
Read More
Zuwan soshiyal midiya ne ya ƙara ruguza kasuwar littafi – Shamsiya Kaduna

Zuwan soshiyal midiya ne ya ƙara ruguza kasuwar littafi – Shamsiya Kaduna

"Babu bangon da muryar rubutu ba ta iya fasawa ba" Daga AISHA ASAS  Manazarta da dama na ra’ayin cewa, marubuta mata ne ƙashin bayan duk wani cigaba da aka samu a duniyar rubutun litattafan adabin kasuwar Kano. Jajircewa da sanin abin da makaranta ke buƙata ne ya sa suka yi wa maza marubuta zarra, har ta kai ko maza 'yan uwansu sun fi karɓar rubutun na mata fiye da nasu. Duk da an tabbatar da cewa, mazan ma ba wai an bar su a baya ba ne, kusan za mu iya cewa, marubuta mata tsintar dami suka yi a kale,…
Read More