Daga IBRAHIM HAMISU a Kano
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da tura sababbin ma’aikatan tsaro na makarantu 1,600 zuwa makarantun sakandare a faɗin jihar, a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa tsaron makarantun jihar.
Matakin ya biyo bayan sace ɗalibai mata 25 da aka yi a Jihar Kebbi kwanan nan.
Gwamnan, a ranar Talata, ya ƙaddamar da rabon takardun ɗaukar aiki na dindindin ga sabbin ma’aikatan.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu, Gwamna Yusuf ya bayyana wannan mataki na tura jami’an tsaron makarantu da yawa a lokaci guda a matsayin “muhimmin mataki wajen dawo da tsaro da daidaito a makarantu.”
Ya jaddada cewa ba za a iya samun ingantaccen karatu ba idan tsaro yana cikin haɗari.
Gwamnan ya ce masu sa-idon za su kasance layin kariya na farko ga ɗalibai, malamai da kayayyakin makaranta ta hanyar sa ido kan zirga-zirgar da ba ta dace ba, daƙile barazanar da ka iya tasowa da kuma tallafa wa ingantaccen gudanar da harkokin karatu.
