Kasashen Waje

Sin ta yi kira ga Amurka da ƙasashen Yamma su soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen ƙaƙabawa

Sin ta yi kira ga Amurka da ƙasashen Yamma su soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen ƙaƙabawa

Daga CMG HAUSA Ƙasar Sin, ta yi kira ga Amurka da ƙasashen yammacin duniya, su gaggauta soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen ƙaƙabawa, da dakatar da keta haƙƙoƙin jama’a a wasu ƙasashe. Wakilin na Sin ne ya yi kiran a jiya, yayin zama na 50 na majalisar kare haƙƙin ɗan Adam ta MƊD, a lokacin da yake halartar tattaunawar da aka yi tsakanin wasu masana masu zaman kansu, a ɓangren haƙƙoƙin bil adama da haɗin giwar ƙasashen duniya. Fassara wa: Fa’iza
Read More
Jami’in Sin: taron shugabannin BRICS ya samu kyawawan sakamako

Jami’in Sin: taron shugabannin BRICS ya samu kyawawan sakamako

Daga CMG HAUSA Shugaban ƙasar Sin Xi Jinping ya jagoranci taron shugabannin BRICS karo na 14 da ya gudana a daren jiya, ta kafar bidiyo daga birnin Beijing, faɗar mulkin ƙasar. Yayin taron manema labarai da aka yi bayan taron, mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Sin Zhao Xu, ya ce taron ya gudanar cikin nasara, wanda ke da muhimmiyar ma’ana ga makomar ƙungiyar. Ma ya furta cewa, a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Xi, shugabannin ƙasashen BRICS sun tattauna sosai kan yadda za a raya kyakkyawar hulɗar abota, a kokarin sa kaimi ga ci gaban duniya. Haka kuma Shugaba Xi ya gabatar…
Read More
BRICS ta fitar da sanarwar Beijing da ta yi alƙawarin kare tsaro da zaman lafiya a duniya

BRICS ta fitar da sanarwar Beijing da ta yi alƙawarin kare tsaro da zaman lafiya a duniya

Daga CMG HAUSA Cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da ta fitar yayin taron kolinta na 14, ƙungiyar ƙasashen BRICS, ta yi alƙawarin kare zaman lafiya da tsaro a duniya. Haka kuma, yayin taron tattalin arziki da kasuwanci na ƙungiyar, an fitar da shirin raya harkokin kasuwanci a ƙasashen BRICS na Beijing, da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da inganta farfaɗowar tattalin arzikin duniya. Mai fassarawa: Fa’iza Mustapha daga CMG Hausa
Read More
Sin za ta ɗauki managartan matakai don cigaba da tallafa wa ajandar cigaba mai ɗorewa ta MƊD nan da 2030

Sin za ta ɗauki managartan matakai don cigaba da tallafa wa ajandar cigaba mai ɗorewa ta MƊD nan da 2030

Daga CMG HAUSA A yammacin yau ne, shugaban ƙasar Sin Xi Jinping ya jagoranci wani babban taron tattaunawa kan ci gaban duniya ta kafar bidiyo, tare da gabatar da muhimmin jawabi. Xi Jinping ya yi nuni da cewa, sai al'ummomin ƙasashen duniya suna rayuwa mai kyau ne kadai za a iya samun ɗorewar wadata, da tabbatar da tsaro, da kare haƙƙin dan-Adam. Ƙasar Sin za ta ɗauki managartan matakai, don ci gaba da tallafawa ajandar samun dauwamammen ci gaba ta MƊD nan da shekarar 2030. Ƙasar Sin za ta kara zuba jari a fannin samar da albarkatu a haɗin gwiwar…
Read More
Kasar Sin ta nuna damuwa kan yadda ‘yan sandan Amurka suka kashe mutane ba bisa doka ba

Kasar Sin ta nuna damuwa kan yadda ‘yan sandan Amurka suka kashe mutane ba bisa doka ba

Daga CMG HAUSA Wakilin ƙasar Sin ya nuna damuwa kan yadda ‘yan sandan ƙasar Amurka suka kashe mutane ba bisa doka ba, yayin da yake tattaunawa da mai sa ido kan batun kashe mutane ba bisa doka ba, a wajen taron kwamitin kare haƙƙin dan Adam na MƊD karo na 50 jiya Laraba. Wakilin ƙasar Sin ya nuna cewa, an sha jin labaru masu tarin yawa dangane da yadda ‘yan sandan Amurka suka ci zarafin wasu yayin da suke aiwatar da doka. An ruwaito cewa, a cikin shekara guda bayan mutuwar George Floyd, wanda ya mutu sakamakon cin zarafi yayin…
Read More
An kammala taron tattauna zaman lafiya na Sin da kusuwar Afrika karo na farko

An kammala taron tattauna zaman lafiya na Sin da kusuwar Afrika karo na farko

Daga CMG HAUSA An kammala taron zaman lafiya da samar da ingantaccen shugabanci da ci gaba na Sin da kusurwar Afrika karo na farko a ranar Talata a Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha, inda aka yi kiran haɗin gwiwa don cimma muradun bai ɗaya na shiyyoyin. Mahalarta taron na kwanaki biyu da aka kammala, sun tattauna tare da fidda sanarwar haɗin gwiwa kan wasu muhimman batutuwa goma sha biyu. Sanarwar haɗin gwiwar ta bayyana cewa, shiyyar kusurwar Afrika wato HOA, wani muhallin zama ne ga al’ummar dake shiyyar, kana ana buƙatar samun tabbatar da zaman lafiyar shiyyar, da kwanciyar…
Read More
CNTAC: Haramcin da Amurka ta sanya wa kayayyakin Xinjiang ya sava dokokin ciniki

CNTAC: Haramcin da Amurka ta sanya wa kayayyakin Xinjiang ya sava dokokin ciniki

Daga CMG HAUSA Ƙungiyar kare muradun kamfanonin samar da tufafi na ƙasar Sin CNTAC, ta ce haramcin da Amurka ta sanyawa dukkan kayayyakin da ake samar a yankin Xinjiang Uygur mai cin gashin kai na ƙasar Sin, ya saɓa wa dokokin cinikayya da tattalin arziki na ƙasa da ƙasa. CNTAC ta ce, tana adawa mai tsanani game da matakin Amurka na haramcin da ta sanya, wanda ba kawai yana haifar da mummunar illa ga moriyar kamfanonin saka tufafi na ƙasar Sin ba ne, har ma zai haifar da illoli ga tsarin dokokin kamfanonin saka tufafi na duniya. A cewar ƙungiyar…
Read More
Ekweremadu da matarsa sun faɗa a komar ‘yan sanda a ƙetare

Ekweremadu da matarsa sun faɗa a komar ‘yan sanda a ƙetare

Daga BASHIR ISAH 'Yan Sanda a birnin London sun tsare tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Dr. Ike Ekweremadu tare da mai ɗakinsa, Beatrice. A cewar jaridar Sky, an tsare su biyun ne bisa zargin haɗin baki wajen ɗebe sassan jikin wani yaro. Sai dai, an ce tuni an ɗauki yaron da lamarin ya shafa zuwa wani wuri don ba shi kariya. Jaridar Sky ta ruwaito cewa, "Ana tuhumar wasu mutum biyu da haɗin baki wajen ɗaukar wani yaro zuwa Birtaniya domin ɗebe wasu sassan jikinsa, in ji 'yan sanda. “An tsare Beatrice Nwanneka Ekweremadu, 'yar shekara 55 da kuma…
Read More
Rahotanni game da kalaman Tedros cewa, Covid-19 na iya ɓulla daga ɗakin gwaje-gwajen Wuhan ba gaskiya ba ne

Rahotanni game da kalaman Tedros cewa, Covid-19 na iya ɓulla daga ɗakin gwaje-gwajen Wuhan ba gaskiya ba ne

Daga CMG Hausa Wasu rahotanni na cewa, a baya-bayan nan babban darektan hukumar lafiya ta duniya (WHO) Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana a asirce cewa, "Mai iyuwa asalin COVID-19 na iya ɓulla daga ɗakin gwaje-gwajen Wuhan." Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen ƙasar Sin Wang Wenbin ya bayyana Larabar nan cewa, sakatariyar hukumar ta WHO ta yiwa ɓangaren ƙasar Sin ƙarin haske, yana mai jaddada cewa, babban darektan hukumar bai furta irin waɗannan kalamai a bainar jama'a ko a ɓoye ba, kuma bayanan da aka bayar gaba daya ba gaskiya ba ne. Babban darektan da kansa bai amince da…
Read More
Sin da Equatorial Guinea sun rattaɓa hannu kan musayar bayanai don taimakawa aikin gona a Equatorial Guinea

Sin da Equatorial Guinea sun rattaɓa hannu kan musayar bayanai don taimakawa aikin gona a Equatorial Guinea

Daga CMG HAUSA A ranar 20 ga wata, a ma'aikatar harkokin waje da hadin gwiwar ƙasar Equatorial Guinea, jakadar ƙasar Sin dake ƙasar Equatorial Guinea Qi Mei da ministan harkokin wajen Equatorial Guinea Simeon Oyono Angue, suka rattaba hannu kan musayar bayanai a madadin gwamnatocin ƙasashen biyu, don taimakawa fasahar aikin gona a ƙasar. Uwar gida Qi Mei ta bayyana cewa, ƙasar Sin tana fatan tallafawa ƙasar Equatorial Guinea, don raya aikin gona na zamani bisa ƙarfin kanta, da inganta ƙarfinta na tabbatar da samar da abinci. A nasa jawabin minista Simeon Oyono Angue ya bayyana cewa, taimakon da ƙasar…
Read More