Siyasa

PDP ta lashe zaɓen Jihar Ribas

PDP ta lashe zaɓen Jihar Ribas

Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar gwamna a Jam'iyyar PDP a Jihar Ribas, Siminialayi Fubara shi ne wanda INEC ta tabbatar a matsayin wanda ya ci zaɓen jihar a zaɓen da ya gudana ranar Asabar da ta gabata. Baturen zaɓe a jihar, Farfesa Akpofure Rim-Rukeh, shi ne ya ba da sanarwar sakamakon zaɓen a ranar Litinin da daddare a Fatakwal, babban birnin jihar. Ya ce Fubara na PDP ya lashe zaɓen ne bayan da ya samu ƙuri'u 302,614, inda ya doke takwaransa na APC, Tonye Cole, wanda ya samu ƙuri'u 95,274. INEC ta ce ɗan takarar SDP, Sanata Magnus Abe, shi…
Read More
Kakakin Majalisar Dokokin Zamfara da mataimakinsa sun dafa ƙasa a zaɓen ranar Asabar

Kakakin Majalisar Dokokin Zamfara da mataimakinsa sun dafa ƙasa a zaɓen ranar Asabar

Daga RABI'U SANUSI a Kano Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Zamfara kums ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Zurmi ta Gabas, Hon. Nasiru Mu’azu Magarya, ya sha kaye zaɓen gwamna da na majalisar jiha da aka gudanar ranar Asabar ɗin da ta gabata. Haka mataimakinsa, Hon. Musa Bawa na Jam’iyyar APC, mai wakiltar mazaɓar Tsafe ta Yamma, bai kai bantensa ba a zaɓen Baturen zaɓen, Mudasiru Samaila, ya ce, Mu’azu ya samu ƙuri’u 13,820 ne a zaɓen, yayin da abokin hamayyarsa na Jam'iyyar PDP, Bello Muhammed ya samu ƙuri’u 21,197. “Don haka ɗan takara Jam’iyyar PDP ne ya samu nasara kujerar Majalisar…
Read More
Zaɓen Gwamna: Lawal ya kwaɓe Matawalle a Zamfara

Zaɓen Gwamna: Lawal ya kwaɓe Matawalle a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Da safiyar Talata Hukumar Zaɓe (INEC), ta bayyana Dr Dauda Lawal-Dare na Jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a Jihar Zamfara. Baturen zaɓen, Farfesa Kassimu Shehu da ya kasance Mataimakin Shugaban Jami'ar Tarayya da ke Birnin Kebbi, shi ne ya sanar da sakamakon zaɓen. Ya ce Lawal-Dare ya lashe zaɓen ne bayan da ya samu ƙuri'u 377,726 daga ƙananan hukumomi 14 a jihar. Wanda hakan ya ba shi famar kwaɓe gwamna mai ci, Bello Matawalle na Jam'iyyar APC daga kujerar Gwamnan jihar. Matawalle ya tsira ne da ƙuri'u 311,976.
Read More
Kefas ya cinye zaɓen Taraba

Kefas ya cinye zaɓen Taraba

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ayyana Kefas Agbu na jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a Jihar Taraba. A cewar INEC, Agbu ya lashe zaɓen ne bayan da ya kere wa takwarorinsa da yawan ƙuri'u 257,926. Hukuma ta ƙara da cewa, ɗan takarar jam'iyyar NNPP, Muhammad Yahaya shi ne ya zo na biyu da ƙuri'u 202,277. Yayin da Emmanuel Bwacha na jam'iyyar APC ya zo ma uku da ƙuri'u 142,502 kamar yadda Naturen zaɓen, Farfesa M.A. Abdulazeez ya bayyana.
Read More
APC ta ci zaɓen gwamna a Kuros Ribas

APC ta ci zaɓen gwamna a Kuros Ribas

Daga WAKILINMU Sakamakon zaɓen da Hukumar Zaɓe INEC ta bayyana a ranar Litinin, ya nuna Jam'iyyar APC ce tablashe zaɓen gwamna a Jihar Kuros Riba. Sanata Bassey Otu shi ne ya lashe zaɓen da ƙuri'u 258,619, inda ya doke babban abokin hamayyarsa na PDP, Sanata Sandy Onor wanda ya tsira da ƙuri'u 179,636.
Read More
Uba Sani ya lashe zaɓen Kaduna

Uba Sani ya lashe zaɓen Kaduna

Daga IBRAHIM HAMISU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ayyana Sanata Uba Sani na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan jihar Kaduna. Sanata Uba Sani dai ya lashe zaɓen gwamnan ne da ƙuri'u 730002, sai mai bi masa na jam'iyyar PDP da ke da ƙuri'a 719196.
Read More
Sheriff na PDP ya doke Omo-Agege na APC a zaɓen gwamnan Delta

Sheriff na PDP ya doke Omo-Agege na APC a zaɓen gwamnan Delta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar INEC ta bayyana Sheriff Oborevwori na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Delta. Wannan ya kasance bisa ga sakamakon da aka sanar a ranar Litinin, Maris 20, 2023, ta Monday Udoh-Tom, Kwamishinan Zaɓen jihar. Udoh-Tom ya ce, Oborevwori ya lashe ƙananan hukumomi 21 cikin 25 da aka haɗa a jihar inda ya kayar da abokin hamayyarsa na jam’iyyar APC, Ovie Omo-Agege. Oborevwori ya samu ƙuri’u 360,234, Omo-Agege ya samu ƙuri’u 240,229, yayin da ɗan takarar jam’iyyar APGA, Chief Great Ogboru ya samu ƙuri’u 11,029. A cikin ƙananan hukumomi 25 da ke…
Read More
INEC ta dakatar da ci gaba da tattara sakamakon zaɓe a jihohin Abia da Enugu

INEC ta dakatar da ci gaba da tattara sakamakon zaɓe a jihohin Abia da Enugu

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ba da sanarwar dakatar da ci gaba da tattara sakamakon zaɓe a jihohin Enugu da Abia. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Kwamishinan INEC, Barista Festus Okoye, ya fitar a ranar Litinin. Wannan na zuwa ne bayan da 'yan baranda suka farmaki ofishin hukumar a yankin Ƙaramar Hukumar Obingwa inda aka yi garkuwa da wasu jami'an zaɓen. A cewar sanarwar, “Hukunar ta yi zama yau Litinin, 20 ga Maris, 2023 inda ta yi nazarin zaɓen gwamna da na majalisar jihar da ya gudana a jihar ranar Asabar, 18 ga Maris,…
Read More
Caleb Mutfwang na jam’iyyar PDP ya lashe zaɓen gwamna a jihar Filato

Caleb Mutfwang na jam’iyyar PDP ya lashe zaɓen gwamna a jihar Filato

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta bayyana Caleb Mutfwang, ɗan takarar jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna na jihar Filato. Wannan sanarwa ta fito ne daga Baturen zaɓe na INEC mai suna Musa Yusuf, bayan kammala qirga ƙuri'un dukka jam'iyyun da suka tsaya takara a zaɓen, wanda ya nuna Mutfwang shi ne da mafi rinjayen quri'u. Mutfwang ya lallasa ɗan takarar jam'iyyar APC, Nentawe Yilwatda. Idan ba a manta ba, da ma ɗan takarar gwamnan na jam'iyyar PDP rahotanni da ma tuni sun nuna shi ke kan gaba wajen yawan ƙuri'un tun…
Read More
Gwamna Zulum ya sake lashe zaɓen gwamna a Jihar Borno

Gwamna Zulum ya sake lashe zaɓen gwamna a Jihar Borno

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Maiduguri Sakamakon da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta sanar na zaɓen Gwamna da ya gudana a jihar Borno a ranar Asabar, ya bayyana Babagana Umara Zulum na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamna da ya gudana a jihar. Da yake bayyana sakamakon da yammacin Litinin, Baturen zaɓen, Jude Rabo, ya ce ɗan takarar jam'iyyar APC, Babagana Zulum, shi ne ya lashe zaɓen da ƙuri'u 545,542. Yayin da babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Mohammed Jajari ya samu ƙuri'u 82,147.
Read More