25
Mar
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jam'iyyar PDP ta dakatar da wasu jiga-jigan mambobinta da suka haɗa da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Pius Anyim, Farfesa Dennis Ityavyar da Aslam Aliyu, bisa zargin katsalandan a harƙallar jam'iyyar. Bayanin Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar na Ƙasa, Mista Debo Ologunagba, a ranar Alhamis. Sanarwar ta kuma cigaba da cewa, “Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na Jam’iyyar PDP ya yi nazari sosai kan al’amuran jam’iyyarmu a ƙasar nan da kuma bin tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin PDP (kamar yadda aka…
