Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya tafi Equatorial Guinea kan ziyarar kwana uku

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

A ranar Laraba ne shugaba Bola Ahmed Tinubu zai fara ziyarar musamman ta tsawon kwanaki uku a ƙasar Equatorial Guinea.

Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Tinubu zai bar Abuja ne a ranar Talata zuwa Malabo, babban birnin ƙasar inda zai gana da shugaban ƙasar, Nguema Mbasogo a Fadar shugaban ƙasa da ke birnin.

A lokacin ziyarar, Tinubu zai tattauna da takwaran nasa kan inganta ababen da ƙasashen biyu suka haɗu a kai ciki har da matsalolin tsaro, mai da kuma gas.

Ƴan rakiyar shugaba Tinubu sune; Ministan harkokin ƙasashen waje, Jakada Yusuf Tuggar da wasu mambobin gwamnatinsa waɗanda zasu shiga cikin ƙulla yarjejeniya kan abubuwa da ke tsakanin Nijeriya da Equatorial Guinea da kuma karfafa alaƙa a tsakanin su.

A watan Maris, 2023 ne Tinubu ya karɓi baƙoncin wakilan Shugaba Nguema a Fadar shugaban ƙasa da ke Abuja inda suka tattauna batutuwan tsaro wanda Nijeriya ta tabbatar da ƙoƙarinta na inganta harkar tsaro na kan gaɓar tekun Gulf na ƙasar Guinea.

By Babaji