Ganduje ya ƙaddamar da kamfanin sarrafa abinci a kano

A Juma’ar da ta gabata Gwamnan Jihar Kano, Umar Ganduje, ya ƙaddamar da kamfanin sarrafa abinci na Mamuda Foods, a yankin rukunan masana’antu da ke Challawa.

Babban Ministan Kasuwanci da Masana’antu, Hon Niyi Adebayo, da Ƙaramar Minitar Kasuwanci, Hajiya Maryam Yalwaji Katagum, su ne suka mara wa gwamnan baya wajen ƙaddamar da kamfanin.