Gwamnatin Tinubu ta ƙara wa ungozomomi alawus zuwa N80,000 daga N20,000

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta amince da ƙarin alawus ɗin shekara-shekara na tufar aiki ga ma’aikatanta da ke aikin ungozomanci a cibiyoyin lafiya daga N20,000 zuwa N80,000.

Hukumar kula da lamuran albashi da kuɗaɗen shiga da sanar da haka a wata wasiƙa da jaridar PUNCH ta samo.

Sabon ƙarin alawus ɗin na nufin an ruɓanya na baya da kaso 300, wanda zai fara aiki daga watan Junairun 2026.

A wasiƙar, wadda ke ɗauke da sanya hannun Shugabanta, Ekpo Nta, hukumar ta bayar da umarnin fara biyan ungozomomin da ke aiki a dukkan asibitocin gwamnati da sabon tsarin ta tsarin biyan albashi na gwamnati, IPPIS.

Hukumar ta ƙara da cewa, daga yanzu ba za a sake biyan su daga rarar kuɗaɗe ba, saidai ana so ne su riƙa samun alawus ɗin da wasu haƙƙoƙinsu kai-tsaye daga tsarin na IPPIS.

Hakan na zuwa ne wattani kaɗan da Ƙungiyar Ungozomomi ta ƙasa (NANM) ta soki tsarin biyan N20,000 a shekara a matsayin kuɗin inifom ga mambobin nata, inda ta ce hakan ya kasa kuma ba babu darajawa acikinsa.

By Babaji