Gwamnoni sun magantu kan dakatar da gwamnan Ribas

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF), ta cigaba da kare matakinta na yin shuru game da abubuwan da ke faruwa a harkokin siyasa a matsayinta na wadda ba ta da ɓangare a ire-iren batutuwan.

A wata takarda da ta fitar a ranar Asabar, NGF ta ce ɗaukar ɓangare a lamuran da suka shafi jam’iyyu ka iya sa kawunan mambobinta su rabu kasancewar su ƴaƴan mabanbanta jam’iyyu.

Hakan ya biyo bayan hukuncin sanya dokar ta-ɓaci a Ribas da Shugaba Bola Tinubu ya yi gami da dakatar da gwamnan jihar da wasu zaɓaɓɓun ƴan siyasa na tsawon watanni shida.

Takardar, wadda ke ɗauke da sanya hannun Darakta-Janar na ƙungiyar, Dakta Abdulateef Shittu, ta ce ƙungiyar ta fi mayar da hankali ne akan harkokin shugabanci da tsare-tsare a madadin rikice-rikicen siyasa da ke tsakanin jam’iyyu.

Bayanin ya biyo bayan kiraye-kiyare ne daga gidajen jaridu na neman NGF ta yi tsokaci game da ababen da ke faruwa a harkokin siyasa a yanzu.

Saidai, NGF ta ce manufofinta sune inganta tsare-tsare da haɗa kai da masu-ruwa-da-tsaki wajen ci-gaban tattalin arziƙi da walwalar al’umma.

Ya kuma tabbatar wa ƴan Nijeriya ƙungiyar za ta cigaba da mayar da hankali wajen shugabanci akan al’amuran da suka shafi ci-gaban tattali da walwalar al’umma.

By Babaji