



Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya isa birnin Landan bisa umurnin da shugaba Tinubu ya ba shi na raka gawar tsohon shugaba, Muhammadu Buhari wanda ya rasu a jiya Lahadi zuwa Nijeriya.
Daga cikin waɗanda suka tarbi Shettima akwai gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum da Ministan Harkokin Waje, Ambasadda Yusuf Tuggar.
