Jamhuriyar Ireland ta koro ƴan Nijeriya 35 ba tare da dalili ba

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Kimanin ƴan Nijeriya guda 35 har da yara ƙanana ne ƙasar Jamhuriyar Ireland ta koro su dawo wa Nijeriya daga filin jiragen sama na Dublin a ranar Laraba.

Irish Mirror ta ruwaito cewa, mutanen sun haɗa da maza guda 21 da mata tara da yara ƙanana biyar, waɗanda suka iso Nijeriya a ranar Alhamis.

Ministan Shari’a na ƙasar, Jim O’Callaghan ya ce ya yi farin ciki da yadda dukkan su suka koma Nijeriya duk da cewa an samu tsaiko a hanya a sakamakon al’amarin lafiya da ya bijiro.

Gwamnatin ƙasar ba ta bayyana haƙiƙanin dalilin koro ƴan Nijeriyar ba, saidai ministan shari’ar ya ce ƙasar tana da dokoki da tsare-tsare na shige da fice don haka yana da muhimmanci a kiyaye su.

Akan haka ne Hukumar Kula da Lamuran ƴan Nijeriya dake Waje (NiDCOM) ta ce ba ta san da batun maido da mutanen ba daga Ireland.

Kakakin hukumar, Abdur-Rahman Balogun ya bayyana wa Punch Diaspora Tales hakan a ranar Alhamis.

By Babaji