Kotu ta ayyana ministan Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen sanata a Filato

Koton Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a Jihar Filato ta soke zaɓen Sanata Napoleon Bali na Jam’iyyar PDP sannan ta ayyana ɗan takarar Jam’iyyar APC kuma Ministan Ƙwadago da Bada Ayyuka, Simon Bako Lalong, a matsayin wanda ya lashe zaɓen Sanatan Filato ta Kudu a jihar.

Kotun ta ce jam’iyyar PDP ba ta da hurumin shiga zaɓen.

Ƙarin bayani na tafe…..