Limamin Masallacin Harami, Sheikh Shuraim ya yi murabus

Daga WAKILINMU

Limamin Masallacin Makka, Sheik Saud bin Ibrahim Shuraim ya yi murabus daga muƙaminsa.

Limamin ya ba da uzurin sake sabunta kwantiraginsa da Fadar Shugaban Ƙasa a ƙarshen watannin 2022 bisa dalilan kansa.

Bayanai sun ce limamin zai iya zuwa ya jagoranci Sallar Tarawi wadda za a tabbatar da shi kafin Ramadan mai zuwa.

Majiyoyi sun ce limamin na da damar sabunta kwantiraginsa a kowane lokaci sannan ya koma kan matsayinsa.

Sai dai babu wani bayani a hukumance daga shugabancin kula da Masallattan Makka da Madina da ke tabbatar da murabus ɗin da Sheikh Shuraim ya yi.

Haka nan, ba a jiyo Fadar Shugaban Ƙasa ta ce komai game da haka ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *