Lukman Ademola ya zama gwarzon ɗan wasan Afrika na 2024

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Ɗan wasan Super Eagles, Ademola Lukman ya lashe kyautar CAF ta shekarar 2024.

An gudanar da taron bada lambobin yabon ne a ranar Litinin, a birnin Marrakech na ƙasar Morocco.

Lukman ya nuna bajinta matuƙa wa ƙungiyarsa ta Atalanta dake ƙasar Italiya a kakar Bara inda ya taimaka mata ta lashe kofin gasar Europa. A wasan ƙarshe ne ya zura ƙwallaye uku a raga.

Ya kuma taka rawar gani wa Super Eagles a gasar kofin ƙasashen Afirka, wato AFCON ta 2024.

By Babaji