Nijeriya ta gaza lashe Kofin AFCON 2023

Spread the love

Daga BASHIR ISAH

A ranar Lahadi aka kammala Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023 inda aka ɓarje gumi tsakanin Nijeriya da Ivory Coast a wasan ƙarshe.

A ƙarshe, Ivory Coast ce ta zo ta ɗaya a gasar bayan da ta doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan ƙarshe na gasar.

Mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware ƙwallon da Nijeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci.

AFCON: Tinubu ya janye aniyyarsa ta zuwa kallon wasan Nijeriya na ƙarshe, ya wakilta Shettima a madadinsa

Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen karshe a garsa AFCON 2023

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware ƙwallon a minti na 62 daga hannun ɗan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

A minti na 81 Sebastian Haller ya ƙara wa mai masaukin baƙi ƙwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023 a inda Nijeriya ta zo ta biyu.

By Editor