Sojojin Amurka sun fitar da bidiyon atisayen da ya yi ajalin mataimakin jagoran ISIS, Al-Manuki

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Sashen Dakarun Sojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ya fitar da bidiyon atisayen sojoji da ya yi ajalin kwamandan ISIS Abu-Bilal Al-Manuki.

A wata sanarwa da AFRICOM ya fitar a ranar Asabar, an ce an gudanar da atisayen ne a ƙarƙashin umarnin Shugaban Amurka da Sakataren Yaƙi da kuma haɗin-gwiwar gwamnatin Nijeriya.

An ruwaito cewa, bincike ya ya nuna cewa an halaka ‘yan ta’adda da dama a yayin harin.

Sashen ya harin ya nufi yankin da akwai taron mambobin ISIS a arewa maso gabashin Nijeriya, inda ya bayyana shi a matsayin wani ɓangare na yaƙi da ta’addanci a yankin Tafkin Chadi.

Al-Manuki na ɗaya daga cikin mayaƙan ISIS da ke aiki tsakanin ƙasa-da-ƙasa a fannin yaɗa labarai da samar da kuɗaɗe da kuma ci-gaba a harkokin samar da makamai, ababen fashewa da tankunan yaƙi.

Ana ɗaukar sa a matsayin ɗan ta’adda mafi aiki a duniya, wanda ya ƙware wajen shirya ƙaddamar da hare-hare da bayar da umarnin garkuwa da mutane.

By Babaji