
Daga BELLO A. BABAJI
Kwamitin kula da Ilimin matakin farko da Hukumomin jarrabawa na Majalisar Wakilai ya bai wa jagorancin Hukumar kula da jarrabawa a Yammacin Afirka (WAEC) wa’adin kwana ɗaya ya hallara a gabansa, wato a yau Juma’a, 30 ga watan Mayu, 2025, domin warware matsalolin da suka dabaibaye jarrabawar SSCE da ke gudana.
Shugaban kwamitin, Oboku Oforji ya bayyana hakan a ranar Alhamis a sakamakon ƙin amsa irin gayyatar a karon farko.
Ya ce, kwamitin ya gayyaci WAEC ne don ya bada ba’asi game da ƙorafe-ƙorafen da ake samu gami da ayyukan da ba su dace ba da ake yi a yayin jarrabawar.
A baya ne kwamitin ya yi aiken saƙon gayyatar ga hukumar, domin zuwa a ranar 27 ga Mayu na neman ta yi bayani gamsashshe ga al’umma akan matsalolin.
Ya koka kan yadda WAEC ta gaza halarta majalisar a ranar da aka tsara, wato 29 ga watan Mayu, yana mai bayyana hakan a matsayin abinda ba za su lamunta ba duba da yadda ya shafi al’umma kai-tsaye.
Ya kuma ce, matuƙar ta ƙi zuwa a ranar Juma’a, to majalisar za ta yi amfani da ƙarfin doka wajen ɗaukar matakin da ya dace.
