Sufeto Janar ya gargaɗi masu raba tallafi ga talakawa bisa rashin tsari

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Sufeto Janar na ƴan sanda, Kayode Egbetokun ya yi gargaɗi game da hargitsi da rashin tsaro da ake samu wajen raba kayayyakin tallafi ga mutane a yayin bikin Kirismas.

Sufeton ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Kakakinsa, Muyiwa Adejobi ya fitar, inda ya ce duk wanda aka samu da sakaci a ɓangarensa yayin irin aikin, za a kama shi da aikata babban laifi.

Egbetokun ya koka kan rashin tsari dake tattare da irin aikin wanda ya haddasa asarar rayuka da dama a Nijeriya musamman a irin wannan lokaci na bukukuwan ƙarshen shekara.

A ranar 18 ga watan Disamba ne wani lamarin alhini ya auku a Ibadan, babban birnin jihar Oyo inda aka rasa rayuka 35 a wajen shaƙatawa waɗanda galibin su yara ne ƙanana.

Haka ma a ranar Asabar a Abuja an rasa rayuka guda 10 da jikkata da wasu suka yi a yayin rabon kayayyakin tallafi a wani cocin katolika dake unguwar Maitama.

Kamar haka ya kuma faruwa a yankin Okija na jihar Anambara wajen rabon kayan tallafi inda mutane 12 suka rasa rayukansu.

Don haka ne Sufeton ya gargaɗi ƙungiyoyi da masu shirya ire-iren ayyukan da su tabbatar da sun yi tsari da zai kula da lafiyar al’umma gabannin su fara aiwatarwa, ya na mai cewa za a hukunta waɗanda suka bijere wa kalaman nasa.

By ukarofi