Wajibi ne Amurka ta cika alƙawarinta

Daga CMG HAUSA

A daren 28 ga wannan wata ne, shugaba Xi Jinping na ƙasar Sin ya tattauna da takwaransa na ƙasar Amurka Joe Biden ta wayar tarho, inda ya yi bayani kan nauyin da ke bisa wuyan ƙasashen Sin da Amurka, ya kuma yi nuni da cewa, Amurka ta yi kuskuren fahimtar dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da kuma bunƙasuwar ƙasar Sin, sa’an nan ya bayyana matsayin ƙasar Sin kan batun Taiwan.

A nasa ɓangaren, Biden ya bayyana fatansa na neman haɗa kai a tsakanin Amurka da Sin, da daidaita sabani yadda ya kamata, ya kuma yi alƙawarin cewa, Amurka ba ta sauya kuma ba za ta sauya manufar “ƙasar Sin ɗaya tak a duniya” ba, ba kuma ta goyon bayan ‘yancin Taiwan.

Wannan ne karo na 5 da shugabannin Sin da Amurka suka tattauna da juna ta wayar tarho, tun bayan Biden ya zama shugaban Amurka. Kana kuma, tattaunawar da shugabannin 2 suka yi a wannan karo, tana da matukar muhimmanci a wannan muhimmin lokaci.

Yanzu haka yaɗuwar annobar cutar COVID-19 da rikicin Ukraine sun kawo tsaiko ga batutuwan ci gaba da kuma tsaro. Yayin da ƙasashen duniya suke fuskantar sauye-sauye da matsaloli, suna fatan Sin da Amurka za su daidaita sabanin dake tsakaninsu yadda ya kamata, za kuma su ba da jagora wajen kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya da ƙara azama kan bunƙasar duniya.

An lura da cewa, a wannan karo, shugaba Xi ya mai da hankali wajen yin bayani kan matsayin ƙasar Sin game da batun Taiwan, wanda shi ne mafi muhimmanci da kuma jawo hankali a fannin hulɗar da ke tsakanin Sin da Amurka. Baya ga haka, a halin yanzu ana ƙara fuskantar barazana a mashigin tekun Taiwan sakamakon wutar da Amurka take ta rurawa.

Wajibi ne Amurka ta fahimci cewa, idan ba ta tinkari batun Taiwan yadda ya kamata ba, to, za a yi illata hulɗar da ke tsakanin Sin da Amurka, wadda ba a taba ganin irinta ba. Amurka ta sha yin alwashin martaba manufar “kasar Sin ɗaya tak a duniya”, da rashin goyon bayan ‘yancin Taiwan, to, wajibi ne ta cika alkawarinta.

Fassarawar Tasallah Yuan