Daga MAHDI M. MUHAMMAD
An samu nasarar kawar da ’yan ta’adda da dama yayin da jirgin yaƙin rundunar sojin sama (NAF) ya saukar da ruwan bama-bamai kan taron dandazon mayaƙan ISWAP.
Rahotanni sun nuna cewa, jirgin yaƙin ya hallaka wasu tare da jikkata da dama a Sabon Tumbun da Jibularam da ke ƙaramar hukumar Marte duk a jihar Borno.
’Yan ta’addan sun gamu da ajalinsu ne ranar Jumu’a, daga harin bama-baman jirgin sojoji, yayin da suke tsaka da gudanar da gagarumin taro tare da sabon shugabansu, Sani Shuwaram.
Ƙarin bayani na nan tafe…