Mataimakiyar gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ta kasance cikin manyan baƙi da suka halarci bikin Hawan Daushe da aka gudanar yau a fadar Sarkin Zazzau a matsayin wani ɓangare na bukukuwan Sallah ƙarama.
Hawan Daushe wata al’ada ce da ke nuna daɗaɗɗen tarihin al’adun masarautar Zazzau, inda manyan jami’an gwamnati, masoya al’adu, masu yawon bude ido da manyan baƙi suka taru domin shaida wannan kyakkyawan biki mai cike da tarihi da al’adu.
Wannan biki, wanda aka saba gudanarwa a rana ta biyu bayan Sallah, ya ƙunshi faretin mahaya dawakai da suka yi ado da ƙayatattun tufafi, tare da rakiyar mawaƙan gargajiya da suka nishadantar da jama’a da kiɗa da waƙoƙin da ke bayyana asalin al’adar masarautar Zazzau.
