Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana yadda ya ƙi amincewa da buƙatar tsohon Gwamnan Legas, Bola Ahmed Tinubu, na zama abokin takararsa a matsayin mataimakin shugaban ƙasa, yana mai cewa bai amince da tikitin Musulmi da Musulmi ba saboda yana ganin hakan bai dace da muradun Nijeriya ba.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata hira da aka yi da shi da harshen Hausa, wadda aka wallafa a shafin ɗ.
Ya ce bayan ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa, wasu dattawa biyar da suka haɗa da Tom Ikimi da Bisi Akande, tare da wasu mutum uku, sun je wurinsa domin sanar da shi cewa Tinubu na son ya zama abokin takararsa.
Atiku ya ce a lokacin ya gaya musu cewa bai dace ya zaɓi Musulmi a matsayin mataimakinsa ba, domin hakan zai haifar da tikitin Musulmi da Musulmi.
“Na gaya musu cewa ba zan iya amincewa da tikitin Musulmi da Musulmi ba, domin hakan ba zai kasance da amfani ga ƙasarmu ba,” inji Atiku.
A cewarsa, Tinubu ya janye daga tafiyarsa tare da shi, inda daga bisani ya goyi bayan marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua.
Atiku ya ce wannan rashin jituwar ita ce ta fara raba siyasarsu, inda suka kasance a sansanonin siyasa daban-daban har zuwa lokacin da suka sake haɗuwa a yakin neman zaɓen Muhammadu Buhari a shekarar 2014.
Atiku ya kuma bayyana cewa bayan Buhari ya lashe zaɓen fidda gwani, ya ziyarce shi a gidansa da ke Abuja domin neman goyon bayansa.
Ya ce Buhari ya sanar da shi cewa ya ci zaɓen fidda gwani, amma yana buƙatar goyon bayansa domin lashe babban zaɓen.
Atiku ya ce ya amince da ba shi goyon baya ne bisa sharadin cewa Buhari ba zai kafa tikitin Musulmi da Musulmi ba.
“Na tabbatar masa cewa zan goyi bayansa bisa sharadin cewa ba zai yi tikitin Musulmi da Musulmi ba. Bayan ya yi tunani na kusan mintuna biyar, ya tabbatar min cewa ba zai yi hakan ba,” inji shi.
A cewar Atiku, bayan Buhari ya bar gidansa, Tinubu ya aika da wasu wakilai domin jin abin da ya faru tsakaninsa da Buhari.
Ya ce Tinubu ya fusata bayan ya fahimci cewa Buhari ba zai zaɓe shi a matsayin mataimakinsa ba, saboda yarjejeniyar da ya yi da Atiku.
Atiku ya ƙara da cewa daga bisani Tinubu ya ba da shawarar cewa Buhari ya zaɓi matarsa a matsayin mataimakiyar shugaban ƙasa, kasancewar ita Kirista ce, amma Buhari ya ƙi amincewa da hakan saboda bai son yin aiki da mace a matsayin mataimakiyar shugaban ƙasa.
A ƙarshe, Atiku ya ce malamai da malaman addini sun shiga tsakani wajen sasanta rikicin, inda aka shawo kan Tinubu ya zaɓi Farfesa Yemi Osinbajo, wanda a lokacin shi ne Babban Lauyan Jihar Legas kuma Kirista, a matsayin abokin takarar Buhari.
Buhari ya amince da zaɓin Osinbajo, inji Atiku.
