Matsalolin tsaro da Nijeriya ke fama da su sun kai wani matsayi mai matuƙar tayar da hankali, yayin da illolinsu ke yaɗuwa a sassa daban-daban na ƙasar. Saboda haka, bai kamata ƙasar ta ci gaba da barin bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa su zama abin da ke raba kan al’umma ko ke gurgunta haɗin gwiwar da ake buƙata wajen tunkarar matsalar tsaro ba.
A saboda haka ne kiran da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi na neman ’yan Nijeriya su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro ya dace da a mara masa baya sosai. Ya isar da wannan saƙo ne a wani taron ƙasa da ƙasa mai taken “Bambance-bambance da Zaman Lafiyar Al’umma: Haɗin Gwiwa Domin Kyakkyawar Makoma”, wanda aka gudanar a Abuja a wannan makon. Babu shakka, saƙon ya zo a lokacin da ya dace.
Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iƙamatus Sunnah (JIBWIS) ce ta shirya taron tare da haɗin gwiwar ƙungiyar ƙasashen Musulmi ta Duniya. Taron ya haɗa jami’an gwamnati, shugabannin addinai da na gargajiya, ’yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki. Haɗuwar waɗannan ɓangarori daban-daban ta nuna cewa bambancin da ke tsakanin ’yan Nijeriya ba lallai ne ya zama rauni ba; idan aka sarrafa shi cikin hikima, zai iya zama ƙarfi.
Ministan ya yi daidai da ya jaddada cewa ya kamata ’yan Nijeriya su fara “tunanin kansu a matsayin ’yan Nijeriya”, su kuma yi aiki tare ba tare da la’akari da bambance-bambancen da ke tsakaninsu ba. Rashin tsaro ba ya tambayar addini, ƙabila ko jam’iyyar siyasar wanda zai shafa. ’Yan ta’adda, ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran miyagu suna barazana ga ’yan ƙasa da al’ummomi ba tare da la’akari da addininsu ko ra’ayinsu na siyasa ba.
Don haka, barin waɗannan bambance-bambance su jagoranci yadda ƙasa ke tunkarar matsalar tsaro na iya ƙara dagula halin da ake ciki. Kamar yadda Hausawa ke cewa, “Hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka.” Nijeriya na buƙatar haɗin kan kowa wajen tunkarar ƙalubalen da ke gabanta.
Haka nan, jawabin Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, Babban Sakataren ƙungiyar ƙasashen Musulmi ta Duniya kuma Shugaban ƙungiyar Malaman Musulmi ta Duniya, ya cancanci a ƙara mayar da hankali a kansa. Kiran da ya yi ga ’yan Njjeriya da su kare mutuntakarsu ta bai ɗaya, tare da yin watsi da yunƙurin mayar da addini, ƙabila da talauci makaman rarrabuwar kai, abu ne da ya kamata a saurara da kyau.
Addini ya kamata ya zama tushen tarbiyya, tausayi, adalci da sulhu, ba kayan aikin zurfafa rarrabuwar kai ba. “Addini na mutum mutuncinsa ne,” don haka bai kamata a mayar da shi wata hanya ta ƙyamatar da ɗan uwa ko tayar da fitina ba.
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, shi ma ya taɓo muhimmin batu wajen jaddada buƙatar ci gaba da tattaunawa, gaskiya, amana da kuma ƙara aiwatar da hanyoyin da za su magance matsalolin ƙasar.
Tattaunawa ba makawa ce a ƙasa mai cike da bambance-bambance kamar Nijeriya. Sai dai tattaunawa kaɗai ba ta isa ba. Taro da jawabai za su rasa amfani idan ba a mayar da shawarwarin da aka cimma zuwa manufofi da ayyukan da za su inganta tsaro, adalci, ilimi da walwalar jama’a ba.
Matsayar Shugaban JIBWIS, Sheikh Abdullahi Bala Lau, cewa gwamnati, ƙungiyoyin addini da al’umma su ƙara haɗa kai ita ma tana da muhimmanci. Musamman ma yadda ya jaddada muhimmancin ilimi da koyar da sana’o’i ga matasa.
Matashin da ba shi da ilimi, sana’a ko wata hanya ta samun abin dogaro da kai na iya zama cikin sauƙin faɗawa hannun masu tsattsauran ra’ayi ko ƙungiyoyin aikata laifuka. Saboda haka, saka hannun jari a matasa ba kawai batun ci gaban tattalin arziki ba ne; wani muhimmin mataki ne na tabbatar da tsaron ƙasa.
Kasancewar manyan jami’an gwamnati, gwamnonin jihohi, shugabannin siyasa, malaman addini da sarakunan gargajiya a wajen taron ya ƙara ƙarfafa wani muhimmin saƙo: tsaron ƙasa ba aikin gwamnati kaɗai ba ne. Jama’a da al’ummomi ma suna da rawar da za su taka wajen gina amana, ƙin kalaman ƙiyayya da kuma tallafa wa ƙoƙarin da ake yi na kawo ƙarshen rashin tsaro.
Wannan ya sa ya kamata ’yan ƙasa su daina kallon tsaro a matsayin abin da ya rataya a wuyan jami’an tsaro kawai. Bayar da sahihan bayanai, ƙin ɓoye masu aikata laifi, da kauce wa yaɗa jita-jita da kalaman da za su iya haddasa rikici duk suna cikin gudummawar da ɗan ƙasa zai iya bayarwa.
Haka kuma, ƙudirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da zaman lafiya da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa, wanda aka bayyana a taron, ya kamata ya kasance tare da ɗorewar matakan aiki a zahiri. Girman Nijeriya da matsayinta a Afirka na nufin zaman lafiyarta ba ta shafi ’yan Nijeriya kaɗai ba; tana da tasiri kai tsaye ga zaman lafiyar yankin Yammacin Afirka baki ɗaya.
Babban saƙon da ya fito daga Abuja a wannan taro a taƙaice shi ne: Nijeriya ba za ta iya kayar da rashin tsaro ba matuƙar rarrabuwar kai ta fara kayar da ’yan Nijeriya.
Haɗin kai ba taken siyasa kawai ba ne; buƙatar tsaron ƙasa ce. Don haka, ya zama wajibi ƙasar ta gina gadoji tsakanin mabiya addinai, ƙabilu da mabambantan ra’ayoyin siyasa, ta kuma tunkari matsalolin da ke gabanta a matsayin al’umma guda mai makoma ɗaya.
Domin kuwa, “idan ƙuda ya haɗa kai, ba ya tsoron gizo.” Nijeriya na da bambance-bambance masu yawa, amma abin da ya fi muhimmanci shi ne ta koyi amfani da waɗannan bambance-bambancen a matsayin ƙarfin gina ƙasa, ba makamin ruguza ta ba.
