‘Yan bindiga sun sace Birgediya Janar Maharazu Tsiga da mutane da dama a Katsina

Spread the love

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina

‘Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun shiga garin Tsiga a ƙaramar hukumar Bakori inda suka kwashe mutane da dama a ciki harda tsohon shugaban hukumar masu yiwa ƙasa hidima Birgediya Janar Maharazu Tsiga.

Wani mazaunin garin da baya so a faɗi sunan sa yace ‘yan bindigan sun kashe ɗan uwan nasu bisa karya dokar su na kada ayi harbi amma yayi ta harbi a gidan Birgediya Tsiga.

Wani mazaunin garin da baya so a faɗi sunan yace basu kashe kowa ba sai da wani ɗan uwan su yan bindigan bayan sun same sa da karya dokar hana yin harbi a cikin gari.

Yace ɗan bindigan da aka kashe yayi ta harbi a gidan Birgediya Tsiga wanda hakan bai masu daɗi ba,”nan take suka harbe shi,suka tafi da gawar.

Ya zuwa yanzu babu wani bayani daga rundunar ƴan sanda ko gwamnatin Jihar Katsina.

By ukarofi