’Yan sanda sun zargi tsohon manajan banki da hannu a fashi

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Rundunar ’yan sandan ta bayyana sunan wani tsohon manajan banki kuma ɗan kasuwa Olufemi Olushakin a wata shari’ar fashi da makami da aka kai gaban wata kotun majistare da ke Ibadan a jihar Oyo.

Olushakin, tare da wasu mutane biyu, an bayyana sunansa ne da laifin yin fashi da makami da aka yi a otel ɗin Global Signature da ke Ibadan da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar 13 ga Disamba.

Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da mutanen biyu, Ayomide Akanni da Daɓid Adewale, da laifuka biyu da suka haɗa da fashi da makami da kuma cin zarafi, yayin da ta bayyana cewa Olushakin yana nan a hannunsu.

A ranar Alhamis, 19 ga watan Disamba, ‘yan sanda sun gurfanar da Akanni da Adewale a gaban babban alƙalin kotun Ibadan, Giwa Babalola, wanda daga bisani ya ba da umarnin a tsare su a gidan yari na Agodi da ke Ibadan.

Ganin cewa kotun majistare ba ta da hurumin shari’ar ‘yan fashi da makami ba, gurfanar da shi wani mataki ne na dakatar da shari’ar domin tabbatar da hukuncin kotu na a ci gaba da tsare waɗanda ake zargin har sai an sake duba ko akwai isassun shaidun da za a gurfanar da su a gaban babbar kotun.

A cewar takardar tuhumar, waɗanda ake zargin sun haɗa baki ne don yin fashi da makami a ranar 13 ga watan Disamba a otal din Global Signature da ke kusa da tashar man fetur ta Enyo, New Gbagi Road, Ibadan, jihar Oyo.

A tuhume-tuhume na biyu, ’yan sandan sun yi zargin cewa waɗanda ake zargin ɗauke da muggan makamai ne suka kai wa manajan otel ɗin, Akinola Dare hari, suka kuma kwace masa sama da Naira miliyan biyu mallakar otel ɗin.

By ukarofi