Daga BASHIR ISAH
Gwamnatin Tarayya ta bayyana ranar 29 ga Maris da 1 ga Afrilu a matsayin ranakun hutun bukukuwan Good Friday da Easter Monday na bana.
Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya bayyana haka a madadin Gwamnatin Tarayya a ranar Laraba.
Ya bayyana hakan ne a ciki wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Aishetu Ndayako.
Tunji-ojo ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga mabiya addinin Kirista da ma ‘yan ƙasa baki ɗaya kan a yi koyi da karantarwa Yesu kamar yadda ya nunar a halin rayuwarsa.