Yayin da ‘yan Nijeriya ke jiran dawowar Shugaba Tinubu, Shettima ya lula Sweden

Spread the love

Daga USMAN KAROFI

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ana sa ran zai tashi daga Abuja a ranar Laraba zuwa Sweden a ziyarar kwanaki biyu don wakiltar Najeriya a tattaunawar Ƙasa da ƙasa.

Stanley Nkwocha, mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Ƙasa, ya bayyana a wata sanarwa cewa ziyarar ta kasance ne bisa umarnin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

“Ana sa ran Mataimakin Shugaban Ƙasa zai dawo gida a ranar Asabar. Yayin da yake Sweden, zai gudanar da tattaunawar Ƙasa da ƙasa tare da manyan jami’an gwamnati, ciki har da ganawa da Amarya Victoria ta Sweden da Firayim Ministan Sweden,” in ji shi.

A yayin ziyarar, Mataimakin Shugaban Ƙasa zai yi amfani da damar wajen binciko hanyoyin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Sweden a ɓangarori masu muhimmanci kamar fasaha, ƙirƙire-ƙirƙire, ilimi, tsarin dijital, sufuri mai dorewa, haƙar ma’adinai da noma.

Sannan zai gana da manyan masu ruwa da tsaki daga ɓangaren gwamnati da kuma masu zaman kansu.

Mataimakin Shugaban ƙasa zai kuma gana da kamfanin Norrsken, wani kamfani na zuba jari da ke Stockholm, wanda kwanan nan ya kaddamar da Norrsken22, wani kuɗin jari na dala miliyan 205 don zuba jari a fannin fasaha.

“Ganawar da za a yi da Norrsken zai bada damar fahimtar yadda ‘yan kasuwan Najeriya za su amfana da wannan kuɗin jari, tare da ƙara ƙarfafa tsarin fasaha a Najeriya.

A cewar Nkwocha, “kamfanoni masu zaman kansu guda 12 daga Najeriya da ke kasuwanci da Sweden za su kasance a cikin tawagar a matsayin wata ƙungiyar masu zaman kansu.

“Yayin da yake Sweden, ana sa ran Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima zai yi magana kan hangen nesa na tattalin arzikin Najeriya da gyare-gyaren da wannan gwamnati ke aiwatarwa domin samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari a Najeriya.”

Wannan ziyarar na faruwa ne a daidai lokacin da wa’adin tafiyar makonni biyu na Shugaban Ƙasa Tinubu ya ƙare.

Tinubu ya bar Najeriya zuwa Birtaniya a ranar 2 ga Oktoba, 2024.

By ukarofi