CAF ta sanar da lokacin gasar AFCON na 2025

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, (CAF) ta ce za’a gudanar da gasar cin kofin Nahiyar Afirka, (AFCON) a tsakanin 21 ga watan Disamba, 2025 da kuma 18 ga watan Janairun 2026 wanda za’a yi a ƙasar, Moroko dake Arewacin Afirka.

CAF ta yanke hakan ne, a yayin wani zaman manyan ofisoshinta da ta saba yi, a ranar juma’a inda ta ce da ta so gudanar da gasar a lokacin bazara ne a cikin shekarar 2025, amma saboda ya haɗu lokacin gasar ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa ta duniya, sai ta mayar da shi zuwa ƙarshen shekarar.

Za’a gudanar da taron shirya jadawalin wasannin a watan Yulin shekararnan, a birnin Johannesburg dake ƙasar Afirka ta Kudu.

Sannan kuma, a watan Satumba zuwa Oktoban 2024 ne za’a buga wasannin hayewa zuwa zagayen rukuni-rukuni na gasar.

By Babaji