
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Rundunar ƴan sanda a Jihar Kogi ta samo gawar Ayo Aiyepeku, wanda ɗan jarida ne a ɓangaren ɗaukar hoto bayan halaka shi da wani abokin aikinsa mai suna Oulwapelumi ya yi.
Kamfanin dillancin labarai ya ruwaito cewa Kakakin ƴan sandan jihar Kogi, Williams Ovye-Aya ya tabbatar da faruwar al’amarin a Lokoja, Babban Birnin jihar, ranar Litinin.
Ya ce, an gano gawar mamacin ne a yammacin ranar Lahadi a wani yanki da ke kusa da ofishin WAEC da ke Crusher Zone 8 a Lokoja.
Daga nan ne aka garzaya da ita zuwa Babban Asibitin ‘Specialist’ a birnin, inda aka fara gudanar da bincike a kai domin gano haƙiƙanin abinda ya faru.
Ya kuma roƙi iyalan marigayin, abokan aiki da ɗaukacin al’umma da su samar musu duk wani bayani da zai taimaka wa binciken nasu.
