Postecoglou ya nemi afuwar magoya bayan Forest

Spread the love

Kocin Nottingham Forest, Ange Postecoglou ya buƙaci magoya baya su kara haƙuri, bayan da har yanzu bai ci wasa ba.

Ranar Alhamis Forest za ta karɓi baƙuncin Midtjylland a Europa League a City Ground a karon farko tun bayan kusan shekara 30 rabon da ta shiga gasar zakarun Turai.

Tsohon kocin Celtic da Tottenham ya maye gurbin Nuno Espirito Santo a watan Satumba, amma har yanzu bai ci wasa ba.

Ya fara da shan kashi 3-0 a gidan Arsenal, sannan Swansea ta yi waje da su daga Carabao Cup da yin canjaras a Burnley da kuma a Real Betis a Europa League na farko a bana.

Sannan kuma Sunderland ta doke ta har gida 1-0 a Premier League a makon jiya.

Tottenham ta kori Postecoglou kwana 16 da ya lashe Europa League.

By ukarofi