Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
An ci gaba da bayyana ra’ayoyi game da ƙarin albashin masu riƙe da muƙaman siyasa da Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga da kuma Kasafin Kuɗi (RMAFC) ke shirin yi.
’Yan Nijeriya da dama da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya a Abuja ranar Litinin sun ce ba yanzu ne lokacin da za a aiwatar da hakan ba.
A cewarsu, shirin ƙarin albashin na zuwa ne a daidai lokacin da akasarin ‘yan Nijeriya ke cikin halin matsin tattalin arziki. Sun ce, ƙarin da aka yi bai dace ba, sun ce hakan ba daidai ba ne.
Masu ruwa da tsakin sun shawarci gwamnati da ta ba da fifiko ga jin daɗin ma’aikata ta hanyar ɗaukar matakan inganta albashi, da gidaje masu sauƙin kuɗi da sauransu.A cewarsu, waɗannan za su taimaka sosai wajen haɓaka ɗabi’ar su, haɓaka aiki, da ingantaccen hidima.
NAN ta ruwaito cewa, hukumar ta bayyana albashin da masu riƙe da muƙaman siyasa ke karɓa a yanzu a matsayin “tsohon abim da bai dace ba ganin yadda shugabannin siyasa ke samun ƙasa da shugabannin hukumomi.
“Shugaba Bola Tinubu yana samun Naira miliyan 1.5 duk wata, yayin da ministocin ke karɓar ƙasa da Naira miliyan ɗaya, alƙaluman da ba su canja ba tun 2008,” inji hukumar.
Dokta Anthony Adeleke, wani kwararren likita a babban birnin tarayya Abuja, ya ce lokacin da ake shirin yin ƙarin kuɗin ba daidai ba ne kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya da dama ke cikin mawuyacin hali.
Adeleke ya ce, dalilan da hukumar ta bayar da shawarar ƙarin albashin bai dace ba, “a gaskiya wannan ƙarin ba lallai bane ta kowace hanya a wannan lokaci.
“Shawarata ga gwamnati ita ce ta ba da fifiko ga jin daɗin ma’aikatan ta hanyar matakan da suka haɗa da mafi kyawun albashi, da gidaje masu rahusa, isassun horar da su na yin ritaya da kuma gaggauta biyan albashi.
“Waɗannan haɓakawa suna da muhimmanci don haɓaka ɗabi’a ma’aikata, haɓaka aiki, da isar da hidima mai inganci,” inji shi.
Rosemary Bolaji, lauya, ta ce ya kamata hukumar ta mayar da hankali kan aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su yi tasiri mai kyau a rayuwar ma’aikata da kuma jama’a.
“Na ji cewa shugaban ƙasa, Bola Tinubu yana karɓar Naira miliyan 18 a ofishinsa a matsayin albashi a duk shekara, wanda ya kai Naira miliyan 1.5 a kowane wata, yayin da ministocin ke karɓar kusan Naira miliyan 1 a kowane wata wanda ya kamata ya zama kusan Naira miliyan 12 a duk shekara.
“Idan da gaske sun karɓi irin wannan adadin, yaya game da malamai, likitoci, ma’aikatan kiwon lafiya da sauran ƙwararrun da suka fi tasiri ga al’umma?
“Waɗannan mutanen da ke yin tasiri ga rayuwar mutane sun fi samun mafi ƙarancin albashi na N70,000, wasu jihohin ma suna fama da biyan albashin ma’aikatansu. Ta ce, “ƙarin da aka samu bai yi la’akari da talakawan da ke fama da ƙuncin rayuwa ba.”
Bolaji ya ce, ɗaya daga cikin ayyukan hukumar shi ne baiwa gwamnatin tarayya da na jihohi shawara kan yadda ake gudanar da kasafin kuɗi da bunƙasar tattalin arziki tare da samar da gaskiya da riƙon amana a harkokin tafiyar da harkokin kuɗaɗen gwamnati.
Ta ce, ya kamata hukumar ta bi aikinta ta hanyar ba su umarni kan yadda za su tafiyar da harkokin kuɗi, maimakon ƙara albashin shugabannin siyasa wanda zai fi cutar da ‘yan Nijeriya.
“Yawancinmu ba ma iya cin abinci sau uku a rana, muna zuwa ofisoshinmu kwanaki biyar na aiki, har yanzu albashinmu gyaɗa ne kawai,” inji ta.
Bolaji ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ba da fifiko kan tsaro da jin daɗin ‘yan Nijeriya, musamman ma’aikatan gwamnati.
A cewarta, abin da na ɗauka shi ne, ya kamata gwamnati ta ƙara samar da hanyoyin samar da tsaro don magance wahalhalu, hauhawar farashin kayayyaki da kuma fatara.
