An ƙaddamar da mataki na biyu na aikin kafa fitilu masu amfani da hasken rana na ba da hannu ga motoci a Abuja

Daga CMG HAUSA

An yi bikin ƙaddamar da mataki na 2 na aikin kafa fitilu masu amfani da hasken rana na ba da hannu ga motoci a birnin Abuja, hedkwatar ƙasar Najeriya jiya Talata 13 ga wata, wanda ƙasar Sin ta ba da gudummowar gudanarwa.

Jakadan ƙasar Sin a Najeriya Cui Jianchun, da babban sakatare a hukumar kula da babban birnin tarayyar Najeriya Abuja Adesola Olusade, da ma wasu jami’an Sin da Najeriya sun halarci bikin.

A yayin bikin, jakada Cui ya ce, aikin yana cikin matakai masu nasaba da manyan ayyuka 9 da aka sanar, a taron dandalin tattaunawar haɗin gwiwa a tsakanin ƙasar Sin da ƙasashen Afirka, kana wani muhimmin ɓangare ne cikin manyan tsare-tsaren haɗin gwiwa a tsakanin Sin da Najeriya.

Sa’an nan kuma, aikin alama ce ta danƙon zumunci a tsakanin ƙasashen 2.

A nasa ɓangare, Adesola Olusade, ya jinjina wa ƙasar Sin, bisa taimakon da ta daɗe tana bayarwa.

Ya ce aikin zai sassauta matsin lambar da ake fuskanta a Abuja, da kyautata zirga-zirgar birnin, da rage yawan haɗarurrukan mota, da kuma sauƙaƙa zaman rayuwar mazauna birnin sosai.

Fassarawar Tasallah Yuan