03
Nov
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon Ministan Sadarwa a gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Adebayo Shittu ya soki ministoci mata a majalisar ministocin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, inda ya bayyana cewa su na saka sutura tamkar ’yan takara sarauniyar kyau. Shittu ya bayyana ra’ayinsa ne a yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, inda ya jaddada muhimmancin jami’an gwamnati su tunkari ayyukansu da muhimmanci. Shittu, wanda ya yi aiki a ƙarƙashin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari daga 2015 zuwa 2019, ya yi waɗannan kalamai ne a matsayin martani ga jawabin da shugaba Tinubu ya…
