02
Nov
"Ya kamata manyan marubuta su kama hannun ƙanana, su yi masu jagora" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zainab Abdullahi Musa mai laqabi da Lailat, matashiyar marubuciya ce daga Jihar Katsina, wacce ta kasance mai himma da kishin rubutun adabin Hausa. Duk da kasancewarta ɗalibar koyon aikin jinya, bai hana ta ware lokaci na musamman don yin rubutun da zai taimaka wajen ilimantar da matasa ƴan'uwanta game zamantakewar rayuwa, da muhimmancin bin iyaye. Kawo yanzu ta rubuta littattafai guda biyar, har yanzu tana cigaba da rubutu. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, marubuciyar ta bayyana masa irin gwagwarmayar da ta sha kafin…
