Editor

9513 Posts
Tun 7 ga wata rayuka na cigaba da salwanta a Gaza

Tun 7 ga wata rayuka na cigaba da salwanta a Gaza

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ba wani babban labari a duniya yanzu da ya sha gaban halin da a ke ciki a yankin Gaza na Falastinawa inda jiragen yaƙin Isra’ila ke cigaba da ruwan boma-bomai kan gine-gine da nuna zummar murƙushe ’yan bindigar HAMAS. Tabbas duk yadda za a iya auna masu rike da bindiga to la shakka sai an tava waɗanda ba ko allura a hannun su. Wani abun damuwa ma shi ne taba ran mata da yara. Bincike ma na nuna hatta jarirai ma ba su tsira ba. Kuma a gaskiya ba a san ranar da yaƙin ko…
Read More
Badaƙala: Yadda Matawalle ya kwashe biliyoyin Naira da sunan gina gidajen saukan Gwamna

Badaƙala: Yadda Matawalle ya kwashe biliyoyin Naira da sunan gina gidajen saukan Gwamna

Gwamnatin Jihar Zamfara ta fitar da sabbin shaidu waɗanda suke fallasa yadda tsohon gwamna kuma ƙaramin minista, Bello Matawalle ya rattaba hannu kan fitar biliyoyin kuɗi don aikin gidajen saukan gwamna. Tsohuwar gwamnatin ta Bello Matawalle ta ƙirƙiri aikin ginawa tare da sayo kayayyaki ga gidajen saukan gwamna a ƙananan hukumomi 14 da ake da su a Zamfara. Wata takardar sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar jiya lahadi a Gusau, ta bayyana cewa takardun da aka fitar suna cikin jerin salsalar fallasa kan irin ɓarnar da Bello Matawalle ya tafka a…
Read More
Ƙarar bindiga ta tarwatsa ‘yan Majalisar Ribas

Ƙarar bindiga ta tarwatsa ‘yan Majalisar Ribas

Daga BASHIR ISAH 'Yan Majalisar Jihar Ribas sun yi rububin neman mafaka don tsirar da ransu bayan da suka ji ƙarar bindiga a wajen majalisar alhali suna tsaka da zama a wannan Litinin. Sabon rikici ya ɓarke a Majalisar Dokokin Jihar Ribas biyo bayan jita-jitar da ake yaɗawa cewa majalisar ta fara shirin tsige Gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara, musamman ganin yadda majalisar ta tsige shugabanta kuma ɗan-ga-ni-kashenin gwamnan, wato Edison Ehie. MANHAJA ta tattaro cewar, Gwamna Fubara a ya yi dirar mikiya da a majalisar da safiyar Litinin inda aka ji harbin bindiga da barkonon-tsohuwa a wajen majalisar, lamarin da…
Read More
Kwamishinan Harkokin Addinai na Jihar Kano: Kwana 100 masu albarka a ofis (1)

Kwamishinan Harkokin Addinai na Jihar Kano: Kwana 100 masu albarka a ofis (1)

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi (SAW). Cikin yardar Allah, a kwana a tashi, mai girma Kwamishinan Addinai na Jihar Kano, ya kusa cika kwana 100 da shiga ofishinsa mai albarka. Domin mai girma Kwamishina Hon Sani Auwalu Ahmed Tijjani ya shiga ofis ne a ranar 3 ga Agusta, 2023, bisa sahalewar Mai Girma Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf. Cikin waɗannan kwanaki da mai girma Kwamishina ya yi a ofis, an gudanar da muhimman ayyuka da suka shafi haɗin kai na musulmi, musamman ƙoƙari da yake yi wajan ganin an samu cikakken…
Read More
Jam’iyyar PDP ta yi babban rashi

Jam’iyyar PDP ta yi babban rashi

Daga BASHIR ISAH Shugabar Mata ta Jam'iyyar PDP ta ƙasa, Farfesa Stella Effah-Attoe, ta rasu. A cewar ahalin marigayiya, ta rasu ne a ranar Lahadi bayan fama da rashin lafiya. Cikin sanarwar da ta fitar ta bakin sakataren hulɗa da jama'a na ƙasa, Debo Ologunagba a ranar Lahadi, PDP ta bayyana rasuwar Effah-Attoe a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya. Sanarwar ta ce a halin rayuwarta, Farfesa Effah-Attoe ta kasance mai himma da ƙwazo wadda ta bada gudummawarta ga cigaban jama'a da ma ƙasa baki ɗaya. Ologunagba ya ƙara da cewa, rasuwar Effah-Attoe ta bar wagegen giɓi a jam'iyyar…
Read More
Makamashi: Duniya labari

Makamashi: Duniya labari

Tare da BASHIR MUDI YAKASI "Duniya Labari," inji masu hikimar zance. Falsafar wannan magana tana tasowa ne 'yayin da wani abu na son zuciya ya fito muraran, sai ka ji an furta wannan kalami, domin tunasarwa cewa wannan al'amari ba sabon abu ba ne, domin ya taba faruwa a wani lokaci baya. Saboda haka za mu yi waiwaye kamar yadda masu nazarce-nazarce ke cewa, "adon tafiya". Duniya ta sami kanta cikin mawuyacin hali na buƙatar makamashi, saboda yawaitar masana'antu a faɗin duniya. Kowacce ƙasa na fafutukar samar da masana'antu domin samar da ababen buƙata ga 'yan ƙasarta da sauran al'ummar…
Read More
Masarautar Argungu ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma’auni

Masarautar Argungu ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma’auni

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Masarautar Kabin Argungu da ke jihar Kebbi ta ɗaura ɗamarar yaƙi da masu tauye ma'auni kan harkokin sayar da abinci a kasuwanni da ke yankin wannan masarautar. Alhaji Abubakar Yaya shi ne Sarkin Bakin Kabi kuma shugaban gudanar da bincike tare da ɗaukar matakin ladabtarwa ga duk wanda aka samu yana tauye ma'auni. A zantawarsa da wakilinmu a cikin rangadin da ye je a kasuwar Bachaka da ke kan iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar ya bayyana cewa ba su yi ƙasa a gwiwa ba wajen yaƙi da masu tauye ma'auni ba saboda wannan aikin ba…
Read More
Sabon Shugaban EFCC ya umarci dukkanin ma’aikatansa da su bayyana yawan kadarorinsu

Sabon Shugaban EFCC ya umarci dukkanin ma’aikatansa da su bayyana yawan kadarorinsu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A matsayin wani ƙwaƙƙwaran mataki na tabbatar da gaskiya da tsaftace hukumar daga ɓatagari, Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin hanci da Rashawa, Ola Olukoyede, ya umurci ma’aikatan hukumar da su gaggauta bayyana kadarorinsu daidai da tanadin doka da ƙa’idojin aikin gwamnati. Ya bayar da umarnin ne a ranar Talata a hedikwatar hukumar da ke Abuja yayin da ya ke jawabi ga manyan ma’aikatan EFCC. Olukoyede ya jaddada cewa yaki da cin hanci da rashawa ya buƙaci waɗanda ke cikin harkar su tsaya kai da fata don cimma nasara. “Dukkanmu za mu bayyana kadarorin mu;…
Read More
Mutum biyu sun tsere daga gidan yarin Katsina

Mutum biyu sun tsere daga gidan yarin Katsina

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani da ake zargin ɗan fashi da makami ne kuma carawon mota ya tsere daga gidan gyaran hali da ke Katsina. Ana tuhumar ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin, Abba Kala da kitsa ayyukan fashi da sace-sacen motoci a Katsina, Filato da sauran jihohin da ke makwabtaka da su. An ce, Kala ya yi amfani da wayarsa ne a lokacin da ake tsare da shi a gidan gyaran hali da ke Katsina wajen shirya wani manaƙisu da aka yi na kwace mota. Kwamandan hukumar gidan yarin ta Katsina Muhammad Abdulmumini Haruna ya tabbatar da faruwar lamarin.…
Read More
Burina na zama ‘yar kasuwa ta ɗaya a tsakanin baƙaƙen fata na duniya – FMK

Burina na zama ‘yar kasuwa ta ɗaya a tsakanin baƙaƙen fata na duniya – FMK

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Hajiya Farida Musa Kallah, mace 'yar kasuwa mai burin ta zama Ɗangote a mata ta ce babban burinta shi ne a ce ita ce ta ɗaya a manyan 'yan kasuwa mata a tsakanin baƙaƙen fata na duniya, kamar yadda Alhaji Aliko Ɗangote ya ke matsayin ɗan Afrika baƙar fata mafi kuɗi a duniya. Hajiya Farida wadda ita ce shugabar kamfanin saye da sayarwa na kayyakin buƙatun yau da kullum na al'umma, ta bayyana haka ne a lokacin taron qungiyar 'yan kasuwa mata ta mu inganta sana'armu wanda aka gabatar a Unguwar GRA dake Kano a…
Read More