29
Oct
Daga UMAR GARBA a Katsina Wasu mahara ɗauke da muggan makamai da ake kyautata zaton ɓarayin daji ne sun hallaka mutum tara, gami da yin garkuwa da wasu mutane da dama a qaramar hukumar ɗan Musa da ke jihar Katsina. Wani mazaunin garin da aka sakaya sunansa, ya bayyana wa MANHAJA cewa maharan waɗanda ba zai iya ƙiyasta yawansu ba, sun afka wa garin cikin daren ranar Lahadi da misalin ƙarfe 8:00 na dare. A cikin mutane tara da suka rasa rayukansu sakamakon harin, har da ɗan sanda da kuma tsohon kantoma na ƙaramar hukumar, wato Hon. Dauda Lawal Mai…
