Editor

9513 Posts
Yunƙurin juyin mulki: Ana musayar wuta a ƙasar Guinea

Yunƙurin juyin mulki: Ana musayar wuta a ƙasar Guinea

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Guinea na nuni da cewa, ana zargin yunƙurin juyin mulki a ƙasar bayan da aka jiyo ƙazamar musayar wuta a Conakry, babban birnin ƙasar, a wannan Asabar ɗin. Shaidu sun shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa, jami'an tsaro sun yi wa yankin ƙawanya, ba shiga ba fita. Wata majiya da aka sakaya sunanta ta ce, “Ana musayar wuta daga tsakanin ɓangarorin da lamarin ya shafa tare da harba makaman yaƙi a Kaloum." “Tun da asuba aka kulle garin, ba shiga, ba fita," in ji wani ɗan kasuwa a yankin. Guinea na ɗaya…
Read More
An kashe masu garkuwa da mutane da ceto mutum huɗu a Kebbi

An kashe masu garkuwa da mutane da ceto mutum huɗu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  A wata arangama tsakanin wani gungun 'yan ta'adda da sojojin bataliya ta ɗaya da ke Birnin Kebbi tare da haɗin gwiwa da 'yan sakai sun samu nasarar kashe 'yan ta'adda da dama tare da ƙwato mutane huɗu da aka yi garkuwa da su a jejin Suru da ke jihar Kebbi. Kamar yadda mai bai wa gwamnan jihar Kebbi shawara kan tsaro Alhaji Abdulrahman Usman ya bayyana, an yi ba-ta-kashi tsakanin jami'an tsaro tare da 'yan sa kai da kuma ɓarayin daji a wata maɓoyarsu da ke  kan tsaunin Bangi a bayan garin Suru inda aka…
Read More
Nijar: An bankaɗo sabbin bayanai kan zargin Bazoum da yunƙurin tserewa

Nijar: An bankaɗo sabbin bayanai kan zargin Bazoum da yunƙurin tserewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumomin shari’ar jamhuriyar Nijar sun sanar cewa binciken da suka gudanar ya bada damar gano wasu ƙarin bayanan da ke gaskanta zargin yunƙurin tserewar Shugaba Mohamed Bazoum da iyalinsa. Sun ce sun kama kuɗaɗe da dama da wasu tarin kayayyaki a fadar ta hamɓararren shugaban. Yayin da ya ke yin bayani a gidan talabijin ɗin RTN mallakar gwamnatin Nijar, mai shigar da ƙara a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta birnin Yamai, Salissou Chaibou, ya ayyana cewa bayanan da suka tattara sun gano cewa an ɗauki hotunan barikin dogarawan fadar shugaban ƙasa da suke zargin hamɓararren shugaban…
Read More
Gwamnan Zamfara ya karɓo wa ‘yan gudun hijira a jiharsa tallafin gaggawa

Gwamnan Zamfara ya karɓo wa ‘yan gudun hijira a jiharsa tallafin gaggawa

Daga BASHIR ISAH Nan ba da jimawa ba 'yan gudun hijira da ma waɗanda rikici ya ɗaiɗaita a Jihar Zamfara za su dara, biyo bayan tallafin da Gwamnan Jihar, Dauda Lawal ya karɓo musu daga Gwamnatin Tarayya. Tallafin gaggawar ya ƙunshi buhunan shinkafa, katan-katan na spaghetti, garin semovita, kayan aikin gona, kekunan ɗinki, kwamfutoci, litattafan rubutu da dai sauransu. A ranar Alhamis da ta gabata Gwamna Lawal ya kai ziyara Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira da Waɗanda Rikici ya Ɗaiɗaita ta Ƙasa don kyautata danganta da kuma nema wa 'yan gudun hijira a jiharsa tallafi kamar yadda mai magana…
Read More
Zan daidaita komai a Man United – Erik ten Hag

Zan daidaita komai a Man United – Erik ten Hag

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Manchester United Erik ten Hag ya ce, aungiyar na cikin wani irin yanayi amma har yanzu yana ganin shi ne mutumin da ya dace ya saita komai a Old Trafford. Nasarar da Newcastle ta samu da ci 3-0 a gasar kofin EFL ita ce babbar nasarar da suka samu a gidan Manchester United cikin shekaru 93. Wannan shi ne rashin nasara na takwas da United ta yi cikin wasanni 15 da ta buga, mafi muni a farkon kakar wasa tun 1962-63. Bayan da United ta sha kashi a hannun Manchester City a ranar Lahadi, shi…
Read More
Jami’an tsaro sun daƙile yunƙurin harin ta’addanci a Kano

Jami’an tsaro sun daƙile yunƙurin harin ta’addanci a Kano

Daga BASHIR ISAH Jami'an tsaro a Jihar Kano sun samu nasarar daƙile yunƙurin harin ta'addanci da Boko Haram ta shirya kaiwa a yankin Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar. Sojoji da DSS ne suka daƙile wannan yunƙuri a ranar Juma'a, tare da kama wasu mutum biyu da ake zargin 'yan ta'adda ne. Cikin sanarwar da ya fitar, mai magana da yawun sojoji, Onyema Nwachukwu ya lissafo wasu makamai da suka ƙwace da suka haɗa da bindiga ƙirar AK 47 guda biyar, bindigar harba roka ɗaya, bom samfurin RPG guda shida, rigunan aiki na sojoji da dai sauransu. Sanarwar ta ƙara da…
Read More
Bikin Magaji bai hana na Magajiya: Matsin tattalin arzikin Nijeriya bai hana Tinubu canza wa matarsa motoci ba 

Bikin Magaji bai hana na Magajiya: Matsin tattalin arzikin Nijeriya bai hana Tinubu canza wa matarsa motoci ba 

Daga AMINA YUSUF ALI  Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana, zai saya wa matarsa Remi motocin Naira biliyan 1.5, kuma shi ma zai sauya motocin ofishinsa da Naira biliyan 2.9. Duk da matsalar rashin kuɗdi da tsadar rayuwar da ake ta kuka, wadda gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ya jefa ‘yan Nijeriya bayan cire tallafin fetur, Tinubu zai sai wa Remi matarsa  motocin Naira biliyan 1.5, shi ma zai sauya motocin ofishinsa da Naira biliyan 2.9. Waɗannan Naira biliyan 2.9 kuwa, Gwamnatin Tinubu za ta kashe su ne wajen maye danƙara-danƙaran motocin Ofishin Shugaban ƙasa, waɗanda aka ci zamanin mulkin…
Read More
Atisaye: Babu buƙatar jama’a su tada hankulansu – NAF

Atisaye: Babu buƙatar jama’a su tada hankulansu – NAF

Rundunar Sojan Sama (NAF) ta yi kira ga 'yan ƙasa kan cewa kada su firgita ko tada hankalinsu da ganin jami'anta bajaja a kan hanyoyi a sassan ƙasa a ranar Asabar. Daraktan Yaɗa Labarai na NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, gudun sassarfa na shekara-shekara na tsawon kilomita 10 da suka saba yi, na bana zai gudana ne a ranar Asabar, 4 ga Nuwamban 2023 da misalin ƙarfe 6.00 a Abuja da sauraran sassan ƙasa inda ake da sansanonin rundunar. Sanarwar ta ce, “Ana shawartar al'umma musamman masu abubuwan hawa da waɗanda ke zama…
Read More
Ƙaramin kasafin kuɗi: Sojojin ruwa sun shafa wa Tinubu kashin kaji

Ƙaramin kasafin kuɗi: Sojojin ruwa sun shafa wa Tinubu kashin kaji

*Ban buƙaci yin ta-more ba, inji Shugaban Ƙasa*Majalisa ta fizgo wa ɗalibai biliyan N5 daga Fadar Shugaban Ƙasa Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu wani ɓangare na ƙaramin kasafin kuɗin da Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta nemi a ba ta cikin ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗi na 2023, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa Majalisar Dokoki, domin neman amincewarta, ya nemi ya shafa shugaban kashin kaji a wajen akasarin masu sharhi da lura da al’amuran yau da kullum a faɗin ƙasar, saboda yadda cece-kuce ya ɓarke akan batun har ma Fadar Shugaban Ƙasa ta magantu kan lamarin. Wannan…
Read More
Duniya mai yayi: Mawakan Kannywood sun yi wa Rarara taron dangi akan Buhari

Duniya mai yayi: Mawakan Kannywood sun yi wa Rarara taron dangi akan Buhari

Daga WAKILINMU Wasu fitattun mawaqan masana’antar Kannywood a ƙarƙashin ƙungiyar mawaƙa ta Murya Ɗaya sun caccakin fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Abdullahi Kahutu, wanda aka fi sani da Rarara, bisa sukar da ya yi wa tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari. Babban abin mamakin shine, yawancin mawaƙan da suka taso su na caccakar Rarara ɗin ba su tare da tsohon shugaban ƙasar a lokacin da ya ke gadon mulki, yayin shi kuma Rarara ɗin yana tare da Buhari har zuwa lokacin da ya sauka daga kan karagar mulki. Rarara ya janyo waccan magana ne a makon jiya, inda ya kira taron…
Read More