03
Aug
Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya rantsar da kwamishinoni da masu ba shi shawara ta musamman su 38 da za su kasance 'yan majalisar zartarwar jihar. A bikin rantsuwar da ya gudana a filin taro na 'Peoples' Square, Katsina, an rantsar da kwamishinoni 20 da masu ba Gwamna shawara ta musamman su 18. A jawabin gwamna Raɗɗa ya hori waɗanda aka rantsar ɗin da su sani cewa amana ce aka damƙa musu, don haka suke da buƙatar su tsare ta kamar yadda Allah Ya buƙata. Gwamnan ya tabbatar musu da cewa ba zai…
