Editor

9513 Posts
Sojojin sun fatattaki ‘yan bindiga a Sakkwato da Zamfara

Sojojin sun fatattaki ‘yan bindiga a Sakkwato da Zamfara

*An kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su Daga BASHIR ISAH Dakarun haɗin gwiwa na rundunar Hadarin Daji mai aikinta a jihohin Sakkwato, Katsina, Kebbi da Zamfara sun fatattaki 'yan bindiga a maɓuyarsu da ke shiyyar Arewa maso Yamma tare da kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su. Kazalika, sojoji sun ƙwace wasu kayayyaki daga 'yan bindigar yayin samamen da suka haɗa da bindigogi da alburusai da babura da shanu da sauransu. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Hedikwatar tsaro ta fitar a ranar Juma'a. Sanarwar ta ce a ranar 3 ga Agusta, sojoji…
Read More
Cire tallafin fetur: Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya a cikin wata biyu – Tinubu

Cire tallafin fetur: Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya a cikin wata biyu – Tinubu

• Ya ce za a raba motocin sufuri 3000 a jihohi• Ya ce sauran abubuwan jin daɗi na zuwa nan ba da jimawa ba Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana a ranar Litinin cewa a cikin ƙasa da watanni biyu Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya sakamakon cire tallafin man fetur. Shugaban ya bayyana haka ne a wani jawabi da aka watsa wa ‘yan Nijeriya kan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a fannin tattalin arziki. “A cikin ƙasa da watanni biyu, mun ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya da za…
Read More
Nijeriya na shirin tura dakarunta Nijar

Nijeriya na shirin tura dakarunta Nijar

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da Majalisar Tarayya a rubuce shawarar ƙungiyar ECOWAS ta bayar na ɗaukar matakin soji s'a kan Jamhuriyar Nijar. Wasiƙar Tinubu ga Majalisar ta ƙunshi har da neman izinin tura sojojin Nijeriya zuwa Nijar kamar yadda ECOWAS ta yanke. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da ya aike wa Majalisar wadda Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanto a zauren majalisar. Sanarwar ta nuna ECOWAS ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubun ta yi tir da matakin juyin mulkin da sojoji suka ɗauka a ƙasar ta Nijar. Ta ƙara da cewa, biyo bayan taron da ECOWAS ta…
Read More
Nijar ta yanke alaƙa da maƙwabciyarta Nijeriya

Nijar ta yanke alaƙa da maƙwabciyarta Nijeriya

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ƙarƙashin jagorancin sojijin juyin mulki, ta sanar da yanke alaƙa da Nijeriya bayan da ƙoƙarin ECOWAS na samar da maslaha a ƙasar ya ci tura. ECOWAS ta bai wa sojojin da suka yi juyin mulkin wa'adin mako guda a kan su maida Mohamed Bazoum kan kujerarsa ko kuma a yaƙe su da ƙarfin soji. A ranar Alhamis da ta gabata Shugaba Bola Tinubu a matsayinsa na Shugaban ƙungiyar ECOWAS, ya tura tawaga ta musamman ƙasar Nijar domin tattauna maslaha. Tawagar ta tafi Nijar ɗin ne ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar (rtd) inda ta gana…
Read More
Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty daga ministocinsa

Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty daga ministocinsa

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty daga jerin waɗanda yake so ya naɗa muƙaman ministocinsa sannan ya zaɓo wasu guda biyu, wato Festus Keyamo da Dr Mariya Mairiga Hakan ya bayyana ne a lokacin da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya karanto wasiƙar da Shugaban Kasa yayin zaman majalisar a ranar Juma'a. Ƙarin bayani na tafe....
Read More
Mashaya za su ɗanɗana kuɗarsu a Nijeriya sakamakon tashin farashin sinadarin giya

Mashaya za su ɗanɗana kuɗarsu a Nijeriya sakamakon tashin farashin sinadarin giya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Masu shan barasa a Nijeriya za su fuskanci matsanancin ƙarin kuɗi, kamar yadda Kamfanin Breweries na Nijeriya (NB PLC) ya sanar da ƙarin farashin kayayyakin sa daga ranar 10 ga Agusta, 2023. Kamfanin NB PLC ya yanke hukuncin ne a wata wasiƙa mai kwanan wata 1 ga Agusta 2023. Kamfanin ya ba da misali da buƙatar sake duba farashin saboda cigaba da hauhawar farashin kayayyaki da kuma wajibcin rage tasirinsa. "Muna sanar da ku cewa za mu sake nazarin farashin barasa daga ranar Alhamis 10 ga Agusta 2023." Yayin da hauhawar farashin kaya ya kai kashi…
Read More
El-Marzuq ya yi murabus daga muƙaminsa a APC saboda hawan Ganduje shugabancinta

El-Marzuq ya yi murabus daga muƙaminsa a APC saboda hawan Ganduje shugabancinta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mai Bai Wa Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Shawara Kan Harkokin Shari’a, Ahmed El-Marzuk, ya yi murabus daga kwamitin zartarwa na jam’iyyar na ƙasa. Majiyar Blueprint Manhaja ta ta samu labarin cewa ya yi murabus ne a ranar Larabar da ta gabata, sakamakon dagewar da wasu abokan aikinsa suka yi na cewa ba zai iya ci gaba da zama a ofis ɗin ba saboda wasu zarge-zargen da ake masa. Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Bisa abubuwan da ke faruwa a cikin babbar jam’iyyarmu ta APC, inda mai girma Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje…
Read More
Tinubu ba zai yi nadamar naɗa ni minista ba, inji Wike

Tinubu ba zai yi nadamar naɗa ni minista ba, inji Wike

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Laraba ne tsohon gwamnan Jihar Ribas Nyesom Wike ya yi alƙawarin cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba zai yi nadamar naɗa shi minista ba. Wike ya bayyana hakan ne a lokacin da ya bayyana gaban majalisar dattawa domin tantancewa. Ya taɓa riƙe mukamin minista a zamanin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan. Da yake tunawa da yawancin ayyukan da ya yi a matsayin gwamna, Wike ya ce: "Waɗannan abubuwan za a iya cimma su idan kun jajirce kuma idan kuna da sha'awar aikin." Ya ce tsofaffin gwamnoni da dama suna sha’awar zama…
Read More
Ko Mbappe zai iya komawa Chelsea?

Ko Mbappe zai iya komawa Chelsea?

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni sun ce ƙungiyar Paris St-Germain ta bai wa Kylian Mbappe wa'adin sabunta kwantiragi a ranar 1 ga watan Agusta ko kuma ya bar ƙungiyar. Ana raɗe-raɗin cewa ɗan wasan na Faransa, mai shekara 24, ya amince ya koma Real Madrid a kakar wasa mai zuwa a kyauta idan kwantiraginsa a PSG ya ƙare. Mbappe na damar barin PSG a kakar bana - ko dai a matsayin aro ko kuma a kan kwangilar dindindin, wanda ta hakan ne PSG za ta iya samun kuɗi a kansa. Sai kuma yanzu ga Chelsea da Barcelona na nuna sha'awar…
Read More
Makamashi: Albarkatun ƙasa a Nijeriya

Makamashi: Albarkatun ƙasa a Nijeriya

Tare Da BASHIIR MUDI YAKASAI Allah Maɗaukakin Sarki ya albarkanci wannan ƙasa ta Nijeriya da albarkatun ƙarƙashin ƙasa, da kusan babu wata a afrika da zata yi gogayya da ita. Kasace da zata taka kowacce irinn rawa a kasuwar duniya a fannin albarkatun ƙarƙashin ƙasa kamar Azurfa da tagulla da tama da kuza da zinariya da lu’u-lu’u da kuma uwa- uba ɗanyan man fetur da gas da kuma dangoginsa. Tun bayan yaƙin duniya na biyu, ƙasar Birtaniya uwar gijiyar wannan ƙasa ta Nijeriya take kwasar wannan garabasar a gurare daban-daban, kamar tama da kuza a yankin Jos a jahar filato…
Read More