15
Jun
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Litinin Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta umarci da a soke rajistar jam'iyyar ADC da wasu jam'iyyu huɗu bisa gazawar cika sharuɗɗan dokar ƙasa akan jam'iyyun siyasa a Nijeriya. Mai Shari'a Peter Lifu, wanda ya yi hukuncin, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta soke rajistar jam'iyyun tunda sun gaza samun kaso 25 na ƙuri'a a babban zaɓen da ya gabata domin biyayya da hukuncin doka. Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa, jam'iyyu biyar da suka haɗa ADC, Accord, AA, APP, da kuma ZLP ne kotun ta…
