08
Jul
Daga UMAR GARBA a Katsina Babbar Kotun Shari’a da ke Katsina ta ba da umarnin tsare Dr. Bashir Kurfi, malami a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, bayan rundunar ‘yan sandan Jihar ta gurfanar da shi bisa zargin vata suna da kuma yaxa bayanan qarya masu tayar da hankali kan gwamnatin jihar. Jaridar Daily Trust ta ruwaito ‘Yan sanda sun ce Dr. Kurfi ya yi iqirarin a wata hira da ya yi a Trust TV cewa Gwamnatin Jihar Katsina ta xauki nauyin wasu ‘yan bindiga zuwa aikin Hajji, zargin da gwamnati ta musanta. Bayan ya musanta laifukan da ake tuhumarsa…
