10
Jul
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun ƙaddamar da hare-hare a sansanonin sojoji guda biyu da ke Maiduguri a Jihar Borno, lamarin da ya yi ajalin mutane uku. Rahotanni sun bayyana cewa, maharan sun kai farmakin ne da misalin ƙarfe 2:14 na daren wayewar Juma'a a sansanin Kofa, kana daga nan suka zarce zuwa wani wajen sojoji a yankin Muna da ƙarfe 2:30. Shaidu da mazauna yankunan da al'amarin ya shafa sun ce maharan sun kutsa ne akan babura, inda suka riƙa harbe-harbe na kan-mai-uwa da wabi, lamarin da ya rikita jama'a…
