12
Jul
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta amince da N50,000 a matsayin sabon ƙayyadadden farashin jarrabawar WAEC da ta NECO ga ɗaliban da ke shirin kammala karatun makarantun sakandare, wanda zai fara aiki daga shekarar 2027. Rahotanni sun bayyana cewa, hakan ya biyo bayan buƙatar da Hukumar Shirya Jarrabawar Ɗaliban Ƙasashen Yammacin Afirka (WAEC) ta gabatar ta neman a ƙara kuɗin jarrabawar kammala sakandare (SSCE) ga ɗalibai. Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da ke ɗauke da kwanan wata; 18 ga Yuni, 2026 da Daraktan Ilimin Babbar Sakandare na Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya, Adeniji Ibrahim ya sanya…
