Babaji

4775 Posts

ICPC ta gurfanar da tsohon minista, Uche Nnaji

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A yau Litinin Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gurfanar da tsohon Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zarge-zargen da suka shafi amfani da takardun karatu na bogi da karkatar da akalar kuɗaɗen al'umma. A cewar hukumar, tuhume-tuhume guda huɗu na da alaƙa ne da zargin amfani da takardun karatu na bogi da bayar da bayanai na ƙarya akan hidimarsa ta ƙasa, yayin da sauran biyun kuma suka shafi karkatar da kuɗaɗe a lokacin da yake minista. Saidai, tsohon ministan ya…
Read More

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin ƙara kuɗin rajistar WAEC da NECO bayan koken al’umma

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirinta na sauya kuɗin rajistar jarrabawar WAEC da ta NECO na 2027, har zuwa lokacin da za ta kammala shawarwari da masu ruwa da tsaki. Rahotanni sun bayyana cewa, Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya ta sanar da matakin a wata sanarwa, inda ta ce ta janye ƙudirin wanda ke ƙunshe a wata takarda da aka fitar a ranar 18 ga Yuni da ke neman yi wa farashin rajistar jarrabawar garambawul. A cewar ma'aikatar, an ɗauki matakin janyewar ne sakamakon samun ƙorafe-ƙorafen al'umma akan matsin da ƙarin kuɗin jarrabawar ka iya…
Read More

Atiku ya caccaki yunƙurin mayar da kuɗin WAEC da NECO N50,000

Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya caccaki rahotannin da ke cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da mayar da kuɗin jarabawar WAEC da NECO zuwa N50,000 ga kowane ɗalibi daga shekarar 2027. A sanarwar da Kakakinsa, Phrank Shaibu ya fitar, Atiku ya ce wannan mataki tare da ƙarin kuɗin makarantun Unity Colleges zai ƙara jefa iyaye cikin wahala tare da hana miliyoyin yara samun ilimi. Ya bayyana cewa, Nijeriya na daga cikin ƙasashen da ke da mafi yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, yana mai cewa ƙara kuɗin jarabawa zai ƙara…
Read More

Kotu ta umarci ‘yan sanda su girke lauya a kowane ofishin rundunar a Nijeriya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kotin Masana'antu ta Ƙasa a Abuja, ta umarci Rundunar 'Yan sandan Nijeriya da ta girke lauya guda a kowane ofishinta da ke sassan ƙasar bisa la'akari da hukuncin kundin dokokin 'Yan sanda na 2020. Mai Shari'a O.Y Anuwe ne ya bayar da umarnin a ranar Juma'a yayin hukunci akan ƙorafin da kwamitin amintattun Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) ya yi akan Hukumar kula da lamuran 'Yan sanda (PSC) da wasu ɓangarori biyar. Haka kuma, kotun ta haramta wa jami'an 'yan sanda da ba mambobin tawagar shari'a ba su riƙa wakiltar rundunar a shari'un fararen…
Read More

An halaka sanannen jagoran ‘yan bindiga, Sani Yello a Zamfara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rahotanni sun bayyana cewa an halaka fitaccen shugaban 'yan bindiga Kachalla Sani Yellow a Ƙaramar Hukumar Anka, wanda ya shahara wajen jagorantar hare-hare, garkuwa da mutane da satar shanu a Jihar Zamfara da wasu sassan Arewa ta Yammacin Nijeriya. Saidai rahotanni sun bambanta kan yadda aka halaka shi, inda wasu majiyoyi suka ce an harbe shi ne a kasuwar Dan Jibga da ke ƙaramar hukumar yayin da ake zargin mabiyan jagoran 'yan bindiga Dogo Gide ne suka farmake shi. Wani rahoton kuma ya ce, an ya nasarar halaka shi ne a wani samamen haɗin-gwiwa…
Read More

Kofin Duniya: Ingila za ta kara da Argentina a wasa dab da na ƙarshe bayan doke Norway

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An tabbatar da wasannin zagayen dab da na ƙarshe na gasar Kofin Duniya ta 2026, inda manyan ƙasashe huɗu suka tsallake zuwa wannan mataki bayan fafatawar da suka yi a zagayen wasannin dab da na kusa da na ƙarshe. Ingila za ta fafata ne da Argentina ranar 15 ga Yuli, 2026. Hakan na zuwa ne bayan doke Norway da ci 2 da 1 yayin da wasan ya kai zangon ƙarin lokaci. Ita ma Argentina ta yi nasarar kaiwa zagayen ne bayan doke Switzerland ta su Granit Xhaka da ci 3 da 1 su ma…
Read More

Gwamna Lawal ya ƙaddamar da matatar sarrafa ma’adinin lithium ta Dala miliyan 200 a Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa ci-gaban al'umma ba zai tabbata ba sai idan ana tafiyar da albarkatun ƙasa cikin gaskiya, adalci da inganci, tare da samar da yanayi mai kyau da zai bai wa masu zuba jari damar gudanar da harkokin su cikin bin doka. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin ƙaddamar da Matatar Haƙowa da Sarrafa Ma'adinin Lithium ta Zamfara da ke ƙauyen Boko, a Ƙaramar Hukumar Zurmi. An gina matatar ne ta hannun haɗin-gwiwar kamfanonin ZAM Mining Company Ltd, Bima Mines Ltd, Jinlide Mining Co. Ltd da wasu abokan hulɗa, kan kuɗin…
Read More

Kisan tubabbun ‘yan ta’adda ba daidai ba ne, inji Sheikh Gumi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen malamin addini, Sheikh Ahmad Gumi ya ƙalubalanci matakin kisan tubabbun mayaƙan 'yan tayar da ƙayar baya, 'yan aware da fursunonin yaƙi, yana mai cewa hakan ya saɓa wa karantarwar addini da hukunce-hukuncen dokokin ƙasa-da-ƙasa. Gumi ya bayyana haka ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce ya dace a riƙa mu'amalantar waɗanda suka miƙa wuya ko janyewa daga rikici bisa doka a madadin ɗaukar matakin hukunci mai tsanani akansu. Malamin ya bayyana cewa wajibi ne a riƙa yi wa shari'a biyayya wajen bin hanyoyin da ta gindaya…
Read More

Jagoran Addinin Iran ya ci alwashin ramuwar mutuwar mahaifnsa

Daga BELLO A. BABAJI Jagoran Addinin Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei ya ci alwashin ramuwar halaka mahaifiyinsa kuma magabacinsa a shugabancin ƙasar, marigayi Ayatollah Ali Khamenei da aka yi a watannin baya, yana mai cewa waɗanda ke da hannu a kisan za su girbi abin da suka shuka. An bayyana haka ne a babban gidan talabijin na Iran a ranar Asabar tun bayan fara jana'izar mahaifin nasa mako guda da ya gabata. A wata sanarwa da aka fitar, jagoran ya ce lallai ba iya Iran kaɗai za ta nemi a adalci akan al'amarin ba, har ma da sauran mutanen duniya, lamarin…
Read More

Gwamnatin Tarayya ta amince da N50,000 a matsayin sabon kuɗin jarrabawar WAEC da NECO daga 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta amince da N50,000 a matsayin sabon ƙayyadadden farashin jarrabawar WAEC da ta NECO ga ɗaliban da ke shirin kammala karatun makarantun sakandare, wanda zai fara aiki daga shekarar 2027. Rahotanni sun bayyana cewa, hakan ya biyo bayan buƙatar da Hukumar Shirya Jarrabawar Ɗaliban Ƙasashen Yammacin Afirka (WAEC) ta gabatar ta neman a ƙara kuɗin jarrabawar kammala sakandare (SSCE) ga ɗalibai. Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da ke ɗauke da kwanan wata; 18 ga Yuni, 2026 da Daraktan Ilimin Babbar Sakandare na Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya, Adeniji Ibrahim ya sanya…
Read More