Assalam alaikum, ina yi wa Edita barka da wannan lokaci. Allah ya albarkaci kamfanin jaridar Blueprint. Wannan batu da zan yi mahana a kai, batu ne mai sosa rai.
A lokacin da ake faman yaƙi da ta’addanci a Nijeriya, sai kuma ga batun kama waɗansu ’yan ci-rani ɗauke da buhunan albarusai da miyagun awayoyi a wata tashar mota a Jihar Legas a aarshen makon da ya gabata.
Waɗanda ake zargin ’yan Arewa ne kuma suna hanyarsu ne kai makaman zuwa yankunansu; Shin me ya sa suka faɗa wannan muguwar sana’a?
Kuma me ya sa a kullum wasu mutane ba su tunanin Allah ne? Mu sani fa duk abin da ka aikata, za ka tsaya a gaban Allah ranar Ƙiyama.
Wasiƙa daga MUSTAPHA MUSA MUHAMMAD, Kaduna. 08168716583/07014606518.