Daga UMAR M. GOMBE
Sabon Shugaban Ƙasar Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum ya naɗa sabbin ministoci da za su yi aiki a gwamnatin sa, kamar yadda sanarwar da Sakataren Gwamnatin ƙasar ta bayyana a ranar Larabar da ta gabata.
Sanarwar ta ƙara da cewa, an naɗa sabbin ministoci 33, kuma shida daga cikin su mata ne. Hakan na nufin adadin ministocin ya ragu idan aka kwatanta da ministoci 43 da suka yi aiki a gwamnatin tsohon shugaba Mahaman Issoufou.
Naɗin ministocin ya faru ne a yayin da sabon Fira Ministan Jamhuriyar ta Nijar Ouhoumoudou Mahamadu ya sha rantsuwar kama aiki.
Ministocin su ne kamar haka:
Ministan Harkokin Waje – Hassoumi Masaoudou
Ministan Ƙasa a Fadar Shugaban Ƙasa – Rhissa Ag Boula
Ministan Tsaro – Alkassoum Indattou
Ministan Cikin Gida – Alkache Alhada
Ministan Koyon Ayyukan Hannu – Kassoum Mahaman Moktar
Ministan Illimi Mai Zurfi – PHD Mamoudou Djibo
Ministan Kiwon Lafiya – Dr Illiassou Idi Mainasara
Ministan Ma’adanai – Mme Ousseini Hadizatou Yacouba
Ministan Sadarwar Hanyoyin Zamani -Hassane Baraze Moussa
Ministan Sufuri – Oumarou Mallam Alma
Ministan Agajin Gaggawa – Lawan Magaji
Ministan Kiwo Kakakin Gwamnati – Tijani Abdukadri
Ministan Gine-Gine – Hamadou Adamou Souley
Ministan Shari’a – Dr Biubacar Hassan
Ministan Yaɗa Labaru da Hulɗa da Sauran Hukumomi – Zada Mahamado
Ministan Kuɗi – Ahmat Jidoud
Ministan Kasuwanci da Masana’antu – Gado Sabo Moktar
Ministan Ayyukan Noma – Dr Alambedji Abba Issa
Ministan Zane-Zane, Gidaje da Tsaftar
Muhali – Maizoumbou Laoual Amadou
Ministan Fasali – Abdou Rabiou
Ministan Man Fetur da Makamashi – Mahamane Sani Mahamadou
Ministan Kula da Al’adu, Yawon Bude Ido da Ayyukan Hannu -Mohamed Hamid
Ministan Inganta Ƙasa da Cigaban Cigaban Karkara – Maman Ibrahim Mahaman
Ministan Kula da Mata Da Kariyar Ƙananan Yara – Mme Allahoury Aminata Zourkaleini
Ministan Illimin Qananan Makarantu – Dr Rabiou Ousman
Ministan Albarkatun Ruwa – Adamou Mahaman
Ministan Qwadago – Mme Ataka Zaharatou Aboubacar
Ministar Muhalli da Yaqi da Kwararar Hamada – Mme Garama Saratou Rabiou
Ministar Kula da Ayyuka da Kariyar Al’umma – Dr Ibrahim Boukary
Ministan Matasa da Wasannin Motsa Jiki – Sekou Doro Adamou
Ƙaramin Minista a Ma’aikatar Kuɗi – Mme Gourouza Magaji Salmou
Ƙaramin Minista a Ma’aikatar Cikin Gida – Dardaou Zaneidou
Ƙaramin Minista a Ma’aikata Harkokin Waje – Youssouf Mohamed Almoktar.