24
Apr
Daga BABANGIDA S. GORA a Kano A cigaba da zagayawa, don ƙara neman goyon bayansa ga al'ummar ƙananan hukumomi 44 da suke Jihar Kano, ɗan takarar kujerar gwamna a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar African Democratic Congress (ADC), Hon. Balarabe Rufa’i, ya alƙawaranta cewa, idan ya samu nasara zai inganta harkar ilimi da yashe dam-dam da ke akwai a jihar don inganta harkar noma da sauransu. Ya ce babu abinda ya fi a yanzu face matasa da sauran al''umma su tashi tsaye don zaɓar wanda zai kawo masu cigaba da canje-canje don cigaban yankinsu da rayuwarsu. Ɗan takarar gwamnan ya kuma ƙudurci…
