29
May
Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Shugaban Majalisar Ƙoli a kan Lamurran Addinin Musulunci a Nijeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa'ad Abubakar ya nuna damuwa akan abinda ya faru a Jihar Anambara na kisan Harira da yaran ta uku. Sarkin Musulmin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin Mataimakin Shugaban Nijeriya Farfesa Yemi Osinbajo yayin wata ziyarar neman goyon bayan wakillan jam'iyyar APC da ke Sakkwato da za su kaɗa ƙuri'un zaɓen wanda zai tsayawa jam'iyyar takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 wato daliget. "Abinda ya faru a jihar Anambara, abu ne na dabbanci na kisan mace…
