15
Jul
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Alhaji Nasiru Nasko Ɗakingari, tsohon ɗan takarar shugabancin Ƙaramar Hukumar Suru a ƙarƙashin Jam'iyyar APC kuma shugaban matasa daga ƙaramar hukumar, tare da matasa sama da 5,000 da ke goyon bayansa, sun bar Jam'iyyar APC zuwa Jam’iyyar PDP ta adawa a Jihar Kebbi. Da ya ke zantawa da wakilinmu a garin Ɗakingari, Alhaji Nasko ya bayyana cewa, ana zaton adalci a APC, amma sai abin ya zama akasin haka wannan ainihi shi ne babban dalilin da ya sanya suka bar jam'iyyar. Ya ƙara da cewa tun da farko sun bayyanawa magoyabayan su da cewa bisa…
